• English
  • Business News
Sunday, October 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
Lai Qingde

Madugun yankin Taiwan na kasar Sin, Lai Qingde (William Lai), ya yi jawabi a kwanakin baya, inda a hannu daya ya nemi jirkita tarihin babban yakin duniya na biyu, da zummar samar da damar balle yankin Taiwan daga kasar Sin. Kana a dayan hannun kuma, ya kururuta batun da ya kira fuskantar barazanar matakan soja daga babban yankin kasar Sin, don neman kara kudin da yankin Taiwan ke kashewa a fannin aikin soja. Sai dai maganarsa ta janyo dimbin suka daga kafofin watsa labaru na yankin Taiwan, inda suka bayyana Lai Qingde a matsayin mai manta tarihin mulkin mallaka da kasar Japan ta yi a yankin Taiwan, wanda kuma ke neman murguda gaskiyar tarihi daga tushe.

 

Sanin kowa ne, komawar yankin Taiwan kasar Sin wani muhimmin bangare ne na sakamakon babban yakin duniya na biyu, da na tsare-tsaren duniya da aka tanada bayan yakin. Kana dimbin kundayen dokokin kasa da kasa sun tabbatar da ikon mulkin yankin Taiwan na kasar Sin. Sa’an nan kuduri mai lamba 2758 da babban taron Majalisar Dinkin Duniya ya zartas a shekarar 1971 ya bayyana manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, yayin da yankin Taiwan ke zaman wani bangare na kasar Sin. Bisa la’akari da yadda Lai Qingde a cikin jawabinsa ke neman jirkita tarihin babban yakin duniya na biyu, da kuduri mai lamba 2758, za mu san cewa shi ne mai cin amanar gaskiyar tarihi, wanda ke neman haifar da illa ga tsare-tsaren kasa da kasa.

 

Sai dai mutanen duniya ba za su taba mantawa da tarihin dan Adam ba, balle ma su bari a jirkita shi yadda aka ga dama. Maganar Lai Qingde da aikace-aikacensa, da tsoma baki da wasu kasashe suke yi cikin batun Taiwan, ba za su taba sauya matsayin yankin na wani bangare na kasar Sin ba, kuma ba za su iya hana dinkewar dukkan yankunan kasar Sin waje guda ba a karshe. (Bello Wang)

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
Daga Birnin Sin

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

October 12, 2025
Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

October 12, 2025
Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Next Post
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d'Or?

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

October 12, 2025
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

October 12, 2025
Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

October 12, 2025
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025
Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba

Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba

October 12, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Kofin Duniya

Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka

October 12, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu

Yanzu-Yanzu: ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki Na Tsawon Mako Biyu

October 12, 2025
Kishi

Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.