• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: “Taron Kolin Dimokuradiyya” Abin Dariya Ne

byCMG Hausa
3 years ago
Dimokuradiyya

Kwanan nan, Amurka ta tsara tare da gudanar da “taron kolin dimokuradiyya” karo na biyu. Duk da cewa a wannan karo, ta hada gwiwa da kasashen Koriya ta kudu da Netherlands da Zambia da ma Costa Rica wajen gudanar da taron, a yunkuri na kara abin da take kira wai “wakilci na dimokuradiyya”, amma ko ta yaya taron zai kasance abin dariya ne kawai. 

Na farko, shi kansa wannan taro babu dimokuradiyya a cikinsa, kasancewar wadanda suka halarci taron ba sabo da son ransu ba ne, kana ba sabo da sun zama abin koyi wajen dimokuradiyya ba, amma sabo da Amurka ce ta zabe su. Wato ke nan ikon Amurka ne. Misali, duk da cewa Turkiyya da Hungary mambobin kungiyar NATO ne, amma ba su samu goron gayyata daga Amurka ba, sakamakon yadda suke yi mata rashin biyayya.

  • Gwamnoni Za Su Gana Da CBN, EFCC, ICPC, FIRS Kan Tattalin Arziki

Na biyu kuwa, Amurka ta gudanar da taron ne ba don dimokuradiyya ba, kasancewar taron mataki ne da Amurka ta dauka don tada yakin cacar baka, wato tana saka wasu kasashe cikin wani rukuni da ma wasu cikin wani na daban, bisa ma’auninta na wai “dimokuradiyya”, don haifar da kiyayya a tsakaninsu.

Na uku, abin dariya ne yadda Amurka ta kasance mai kiran wannan taro, kasancewar kasar ta kawar da idonta daga matsalolin hakkin bil Adam da take fuskanta a cikin gida, inda ake ta fama da matsalolin wariyar launin fata da harbe-harben bindiga da dai makamantansu, kuma kwanaki biyu kafin taron, an sake jin karar bindiga a wata makaranta da ke jihar Tennesse, lamarin da ya kai ga halaka mutane da dama, amma ga shi shugaban Amurka ya halarci taron tamkar babu abin da ya faru ba. Baya ga haka, Amurka ta kuma yi ta lalata dimokuradiyya a waje, inda ta tilasta sauran kasashen duniya su yi na’am da ra’ayoyinta na dimokuradiyya, tare da nuna fin karfi, ga kuma munanan laifukan da ta aikata a kasashen Afghanistan da Iraki da Syria, amma kuma tana daukar kanta a matsayin mai koyar da dimokuradiyya a duniya.

Dimokuradiyya ba abin ado ba ne, a maimakon haka, ya kamata ya kasance abin da zai taimaka wa al’umma wajen daidaita matsalolin da suke fuskanta. Dimokuradiyya mai inganci tana taimakawa wajen gudanar da harkokin kasa da ma raya kasa yadda ya kamata, a maimakon ta zama “misali” ga duniya amma ga tarin matsalolin da ake fuskanta a gida. Baya ga haka, ya kamata dimokuradiyya mai inganci ta taimaka wajen hada kawunan al’umma a maimakon ta haifar da rarrabuwar kawunansu, kuma ta taimaka wajen kiyaye kwanciyar hankalin al’umma a maimakon ta haifar da tashin hankali. Amma idan mun yi nazari a kan da yawa daga cikin matakan da Amurka ta dauka a fagen duniya cikin ‘yan shekarun byaa, za mu gano cewa, tana maganar “dimokuradiyya” ne kawai a fatar baka, amma ba tare da mayar da hankali kan batun bunkasuwar kasa da kasa ba. To, da haka za mu fahimci cewa, tana daukar dimokuradiyya ne a matsayin abin ado kawai, wanda ba zai haifar da alfanu ga al’ummarta da ma kasashe masu tasowa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Amurka dai tamkar wasa take yi wajen gudanar da “taron kolin dimokuradiyya”, don haka ma taron zai zama shirme kawai wanda ba zai haifar da da’a mai ido ba. (Lubabatu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Next Post
Abba Na Kokarin Fara Mulkin Kano Da Kuskure —Ganduje

Abba Na Kokarin Fara Mulkin Kano Da Kuskure —Ganduje

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version