Sakamakon yadda ake fuskantar karancin ruwan sama a jihar Borno, a wannan damina ta bana, Mai Martaba Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai Elkanemi, ya bukaci al’ummar musulmi a jihar da su fita rokon ruwa.
A don haka, Shehun Borno, ya bukaci al’ummar musulmi a jihar su fito kwansu da kwarkwata domin yin addu’o’in rokon ruwa ga Allah Madaukakin Sarki.
- Zulum Ya Kaddamar Da Kwalejin Ilimi Ta Farko A Jihar BornoÂ
- Musabbabin Haramta Sana’ar Gwangwan A Jihar Borno
Shehu ya sanar da hakan a wata sanarwar manema labaru mai dauke da sa-hannun Sakatarensa, Zannah Umar Ali, inda ya bayyana cewa za a gudanar da sallar rokon ruwan ta raka’a biyu, yau Litinin a filin kare gudunka na Ramat Square dake Maiduguri, da misalin karfe 10:00 na safiya.
Har wala yau, sanarwar ta bukaci al’ummar musulmi; maza da mata, yara da kanana tare da dattawa masu yawan shekaru don halartar sallar rokon ruwan, da neman taimakon Allah wajen samun ruwan sama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp