• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi tir da Allah wadai da kisan da sojoji suka yi wa masu maulidi da cewa hakan kan ya faru ne bisa ‘kuskure’, inda ya misalta hakan da babban sakacin da bai kamata ya faru ba. 

Dahiru Bauchi a saƙon jajensa da ya aike wa musulman duniya kan kisan masu Maulidi kauyen Tudun Biri da ke ƙaramar hukumar Igabi a Kaduna da ake zargin mutum kusan 85 sun rasa rayukansu yayin da wasu sama da 50 suka jikkata a daren ranar Lahadi yayin da suke zaman tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad wato Maulidi.

  • Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan N207.75bn A Matsayin Kasafin 2024

Shehin ya bukaci gwamnati da ta gabbata kafa kwamitin bincike da zai gano waɗanda suka aikata hakan domin hukunta su.

A cewarsa, koda sojojin sama sun ce ba su da masaniya kan kisan, amma alhakin kula da yaƙi ta sama na wuyarsu don haka su ma akwai sakacinsu, ya kuma dora laifin ga sojojin sama da na kasa da kuma gwamnati.

Kazalika, babban malamin darikar ya nemi gwamnati ta biya diyyar masu maulidin da suka rasa rayukansu sakamakon ruwan bama-bamai da sojoji suka yi musu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

A cewarsa: “Ina yin ta’aziyya ga dukkanin musuluman duniya da musulman Afrika da musulman Nijeriya a kan abun da ya faru, wanda ya faru a Kaduna mun bincika sun ce wai ba jiragen saman sojojin Nijeriya ba ne, sojojin kasan Nijeriya ko sun ce su ne, to ai su babu dama su hau sama. Saboda haka mun yi mamakin yadda aka rasa rayuka.”

Ya ce, babban mai laifi kan wannan lamarin ita ce gwamnati domin ita ce ta yi sake.

“Haƙiƙa mun ji zafi! mun ji zafi!! kuma muna yin ta’aziyya ga dukkanin musulmai na duniya bisa ga wannan rashin da muka yi.”

“Mun kuma yi mamakin yadda sojojin saman Nijeriya suka ce ba su san da harin ba, mun yi mamaki yadda suka hau soma suka sako bam kan mutane. Mun yi mamakin yadda aka kona kusan mutum dari. Wannan hakika ya yi yawa.”

Ya ce, wannan babban sake ne da ya kama tun daga kan sojojin sama domin a cewarsa su ne ke da alhakin kula da yaƙin sama, da su kansu sojojin kasan hadi da ganin laifin gwamnati kan harin da ya farun.

Ya yi kira ga gwamnati da ta gaggauta kafa kwamiti domin binciko ta yadda lamarin ya faru da har aka kashe mutane kusan 100.

“Muna neman su sanar da mu yadda aka ƙona mana masu maulidi a jirgin sama. Mun ji zafi matuka. Gwamnati tana nan tana kallo aka yi wannan abun a gabanta, don haka muna neman ta biya diyya na mutanenmu masu maulidi,” Sheikh Dahiru ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron SGI Na Gudana Kan Sauyin Yanayi Karo Na 28

Next Post

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

42 seconds ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

14 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

15 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

16 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

18 hours ago
Next Post
Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.