Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC), ta bayyana shekarar 2024 a matsayin shekarar da ta fi fuskantar kalubale ga ma’aikata a kasar.
Shugaban kungiyar NLC, Joe Ajaero ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Abuja a wani taron Makarantar Harmattan ta 2024, mai taken “Kungiyoyin Kasuwanci da Neman Sabuwar Kwangila ta Zamantakewa.”
- UNESCO Ta Sanya Karin Al’adun Gargajiya 3 Cikin Jerinta Na Al’adun Gargajiya Da Ba Na Kayayyaki Ba
- Sin Ta Aike Da ‘Yan Sandan Kwantar Da Tarzoma Sama Da 2,700 Daga Shekarar 2000
A cewarsa, shekarar 2024 ta cika da tsananin wahala ga ma’aikata a kasar nan.
“Ina maraba tare da ku na ganin shekarar da muke ciki wadda muka shaida daya daga cikin mafi girman tashin hankali a tarihinmu na masu gwagwarmaya. Lokaci ne da aka kai ta mana yaudara, an kuma yi mana barazana da tsoratarwa,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp