• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shettima Zai Kaddamar Da Cibiyar Horaswa Da zaƙulo Hazikan Matasa A Gombe

Shirin Guraben Ayyuka 2,000 Ga Matasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Shettima

Jihar Gombe ta shirya karɓar baƙuncin Mataimakin Shugaban Nijeriya, Sanata Kashim Shettima, a ranar Litinin inda zai ƙaddamar da shirin samar da guraben ayyuka da janyo masu zuba jari daga waje (OTNI) tare da ƙaddamar da Cibiyar Horaswa da zaƙulo Hazikan Matasa (BPO). 

Cibiyar ta BPO wacce ita ce ta farko a shiyyar Arewa Maso Gabas kuma irinta mafi girma a Nijeriya, an tsara zata samar da aƙalla guraben ayyukan yi 2,000 ga matasa masu basira da hazaƙa a Jihar Gombe bisa irin jagorancin hangen nesa na Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

  • Tsokaci Kan Yadda Matsin Rayuwa Ke Sa Wasu Mata Da ‘Yan Mata Aikata Fasadi
  • Gwamnatin Kano Na Shirin Dawo Da Sheikh Daurawa Kujerarsa Ta Hisba

Yanzu da aka kafa cibiyar ta BPO a Gombe, a Cibiyar Horar da Sana’o’i ta Amina Mohammed Skills Acquisition Centre da ke Bypass daura da hanyar Gombe zuwa Biu, jihar ta shirya zama cibiyar samar da kayayyaki, ta hanyar amfani da basira da hazakar matasanta.

Cibiya irin ta OTNI, hanya ce dake kawo sauyi a harkar kasuwanci da samar da fasahar ƙere-ƙere, kuma hanya ce mafi sauri da za ta samar da ayyukan yi ga matasan Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

A cewar sanarwar da Ismaila Uba Misilli, Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe ya fitar, ta hanyar shiga wannan shiri, gwamnatin Gwamna Inuwa Yahaya ta ƙara nuna aniyarta na samar da ayyukan yi masu ɗorewa da baiwa matasa damar bada gudumawa mai ma’ana ga ci gaban jihar.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Misilli ya ce, “Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya yana miƙa godiya ga Mai Girma Mataimakin Shugaban Ƙasan Kashim Shettima bisa goyon baya da jajircewansa wajen bunƙasa tattalin arzikin Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya, a daidai lokacin da yake shirin karɓar baƙuncin mataimakin shugaban ƙasan da sauran baƙi.”

“Taron ƙaddamarwar zai gudana ne a ɗakin taro na ƙasa da ƙasa dake kan hanyar Gombe zuwa Bauchi da misalin ƙarfe 9:00 na safe, wanda zai samu halartar manyan masu ruwa da tsaki na gwamnati da masu zaman kansu daga ciki da wajen kasar nan.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Next Post
Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.