• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Buhari Ya Karrama CGI Isah Jere Da Lambar Yabo Ta Ƙasa Bisa Mutunta Ɗan’adam A Shugabancinsa

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Buhari

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya karrama Kwanturola Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS), CGI Isah Jere Idris da lambar yabo ta ƙasa “Member of the Order of the Federal Republic (MFR)” a yau 11 ga Oktobar 2022, a Babbar Cibiyar Taro ta Duniya da ke Abuja.

  • Mauludi: Buhari Ya Bukaci ’Yan Siyasa Su Guje Wa Amfani Da Kalaman Batanci

An karrama shi da lambar yabon ne bisa la’akari da yadda yake mutunta ɗan’adam a tsarin shugabancinsa da kuma namijin ƙoƙarin da yake yi wajen haɓaka ayyukan NIS a matsayin ɗaya daga cikin hukumomin kula da shige da fice na duniya mafi ƙwazo da iya aiki musamman ta fuskar kula da kai-komo da tsaron iyakokin ƙasa.

NIS
Sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, Amos Okpu ya fitar ga manema labarai ta bayyana cewa, har ila yau Babban Mataimakin Kwanturola Janar mai kula da sashen bayar da biza da takardun zaman baƙi a cikin ƙasa, DCG Isiaka Abdulmumuni Haliru shi ma ya samu lambar yabon ta MFR daga shugaban ƙasa a gagarumin bikin da ya samu halartar hamshaƙan mutane.
Bikin bayar da lambar yabon dai ya kasance abin alfahari ga NIS saboda baya ga Kwanturola Janar na yanzu da ɗaya daga cikin manyan mataimakansa da suka samu lambar yabon, har ila yau akwai tsofaffin shugabanninta, Martins Kure Abeshi da Muhammad Babandede da su ma aka karrama su.

NIS
An bai wa Abeshi lambar MFR, shi kuma Babandede aka ba shi OFR. Wakazalika, akwai tsohuwar mataimakiyar Kwanturola Janar, DCG Anthonia Ifeoma Opara mai ritaya da ita ma aka karrama da lambar MFR.

NIS
Sanarwar ta ce shugabanni da sauran jami’an NIS na taya Kwanturola Janar Isah Jere Idris da sauran waɗanda aka karrama murnar lambobin yabo na ƙasa da suka samu, tare da yi musu fatan ƙarin ƙoshin lafiya da gudunmawa wajen gina ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Karya Ne Ba’a Sace Wayar Namadi Sambo A Ganganin Yakin Neman Zaben APC Ba —Keyamo

Karya Ne Ba'a Sace Wayar Namadi Sambo A Ganganin Yakin Neman Zaben APC Ba —Keyamo

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.