• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauka Abuja bayan ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai a ƙasar Ƙatar.

Jirgin shugaban ƙasa, mai lamba NAF 001, ya sauka a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da misalin ƙarfe 7 na dare.

  • Nijeriya Da Qatar Sun Rattaba Hannu Kan Yarjeniyoyi Daban-Daban
  • Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Tinubu ya kammala ziyararsa zuwa ƙasashen waje karo na 12 tun bayan da ya karɓi ragamar shugabancin ƙasar watanni tara da suka gabata, kuma ya yi kwana 75 a ƙasashen waje.

Tinubu ya samu tarba daga manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima; Shugaban Ma’aikatan sa, Femi Gbajabiamila; Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume; Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike; Shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Ganduje; da Darakta Janar na Hukumar Tsaro, Yusuf Bichi, da dai sauran su.

A ranar farko ta ziyarar tasa, shugaban na Nijeriya ya ziyarci gidan adana kayan tarihi na Ƙatar inda ya jaddada muhimmancin rubuta sahihin bayanan tarihin ƙasa, da al’adu, da cigaba, da ƙalubale.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Da yake rangaɗin jibgegen ginin wanda ya kai murabba’in mita 39,994 da ke kewaye da asalin fadar Sheikh Abdullah bin Jassim Al-Thani, shugaban ya ce, “Yana da kyau a rubuta al’adu tun farkon tarihi, al’adun wayewa, haɗin gwiwa, ƙalubale da jajircewar shugabanci.”

Washegari, Tinubu tare da Sarkin Ƙatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani sun shaida rattaba hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi guda bakwai a tsakanin ƙasashen biyu, bayan ganawar sirri da suka yi a fadar shugaban ƙasa dake Doha.

Sun haɗa da: yarjejeniyar haɗin gwiwa a fagen ilimi; sanya ƙa’idojin ɗaukar ma’aikata tare da gwamnatin Ƙatar; kafa majalisar hada-hadar kasuwanci tsakanin Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa da Masana’antu ta Ƙatar da Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa da Masana’antu da Ma’adinai da Noma ta Najeriya; baya ga yarjejeniyar haɗin gwiwa a fagen matasa da wasanni.

Sauran yarjejeniyoyin sun haɗa da haɗin gwiwa a fannin yawon buɗe ido da harkokin kasuwanci, da kuma yarjejeniyar fahimtar juna da ke yaƙi da haramtacciyar fataucin miyagun ƙwayoyi.

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, da jami’an gwamnatin Ƙatar, Buthaina bint Ali Al Jabr Al Nuaimi, Ministar Ilimi da Ilimi Mai Zurfi; Dr. Ahmad Hassen Al-Hammadi, Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje; Sheikh Khalifa Bin Jassim Al Thani, Shugaban Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Ƙatar da Abdullah bin Khalaf bin Hattab Al Kaabi, Mataimakin Sakatare na Ma’aikatar Cikin Gida ne suka sanya hannu kan takardun.

A ranar Lahadi ne Tinubu ya jagoranci Taron Kasuwanci da Saka Hannun Jari na Najeriya da Ƙatar inda ya buƙaci shugabannin masana’antu na Ƙatar da su kai rahoton duk wani jami’in Najeriya da ya nemi cin hanci kafin a bar su su yi kasuwanci a ƙasar.

Ya nanata cewa Najeriya ba zai ƙi cigaba ba saboda abubuwan da suka faru a baya da ke cike da jinkiri na gwamnati da cin hanci da rashawa da ke daƙile sauƙin kasuwanci.

“Kada ku ba da cin hanci ga kowa daga cikin jama’armu. Za ku sami damar zuwa gare ni, ” inji Tinubu.

Shugaban ya kuma tabbatar wa da ‘yan kasuwar duniya cewa Nijeriya a shirye take ta gudanar da harkokin kasuwanci da gaske domin gwamnatin sa za ta yi maganin duk wata maslaha a ƙasar da ke kawo cikas ga masu zuba jari a tattalin arziƙin Najeriya.

Ya kuma yi alƙawarin kawar da duk wasu matsaloli da ke kawo cikas ga harkokin kasuwanci yana mai cewa, “Kada ku bari hasashe ya zama cikas ga shirin ku na saka hannun jari. Nijeriya da gaske take game da kawo sauyi a fannin zuba jari.”

Ƙatar dai ita ce ƙasa ta uku a yankin Gulf da Tinubu ya kai ziyara tun bayan da ya ɗare kujerar shugabancin ƙasar da kuma ziyarar sa ta 16 a ƙasashen waje.

Ya zuwa yanzu, ya ziyarci birnin Paris na ƙasar Faransa (sau uku); Landan, Birtaniya; Bissau, Guinea-Bissau (sau biyu); Nairobi, Kenya; Porto Norvo, Jamhuriyar Benin; New Delhi, Indiya; Abu Dhabi da Dubai a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa; New York, Amurka, Riyadh, Saudi Arabia, Berlin, Jamus da Addis Ababa, Habasha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin shugaba TinubuZiyarar Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 

Next Post

Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

Related

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

29 minutes ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

3 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

4 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

5 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

6 hours ago
Next Post
Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.