• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Jinping Ya Yi Kira Da A Inganta Hadin-Gwiwa Ta Hanyar Gudanar Da Wasannin Motsa Jiki

by CMG Hausa
2 years ago
Xi Jinping

An kaddamar da gasar wasannin motsa jiki ta daliban jami’o’in kasa da kasa a lokacin zafi karo na 31, da daren jiya Jumma’a 28 ga watan nan a birnin Chengdu, na lardin Sichuan na kasar Sin, inda shugaba Xi Jinping ya halarci bikin kaddamar da gasar. 

Rahotanni na cewa, ‘yan wasannin motsa jiki 6500, daga kasashe da yankuna 113 ne za su fafata a wasanni daban-daban. Manufofin gasar sun hada da sada zumunci, da kauna, da adalci, da tsayawa bin gaskiya, da hadin-gwiwa, da kuma nuna kwazo, manufofin da a ganin shugaba Xi, ba kawai suna samar da alkibla mai kyau ga fannin tunani ga wasannin motsa jiki na daliban jami’o’in kasa da kasa ba ne, har ma suna samar da misalai, ga shawo kan manyan sauye-sauye na duniya a wannan zamanin da muke ciki.

  • Mukaddashin Shugaban FISU: Shirin FISU Na Inganta Lafiyar Dalibai A Makarantu Ya Yi Daidai Da Ra’ayin Shugaba Xi Jinping A Fannin Raya Kasa Ta Hanyar Motsa Jiki

A wajen liyafar maraba da zuwan baki birnin na Chengdu, shugaba Xi ya gabatar da jawabi, wanda a cikin sa yake cewa, ya dace a inganta hadin-gwiwa ta hanyar gudanar da wasannin motsa jiki, don sanya kuzari ga kasa da kasa. Kaza lika ya kamata a zama tsintsiya madaurinki daya, domin shawo kan kalubalolin kasa da kasa, ciki har da sauyin yanayi, da karancin abinci, da ayyukan ta’addanci da sauransu, a wani kokari na kirkiro makoma mai haske. Al’amarin da ya bayyana ra’ayinsa na gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya, wanda kuma ya wakilci ra’ayoyi bai daya na dan Adam.

Har wa yau, shugaba Xi ya bayyana kyakkyawan fatansa ga matasan kasa da kasa, inda ya ce, yana fatan za su kalli duniya mai cike da mabambantan al’adu, bisa ra’ayoyin nuna adalci da hakuri da kauna, da kara fahimtar al’adu iri daban-daban bisa ra’ayin yin koyi da juna, a wani kokari na bayar da tasu gudummawa, wajen shimfida zaman lafiya da samar da ci gaba a duniya. (Murtala Zhang)

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna

’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.