• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

by CGTN Hausa
2 years ago
CMG

A ranar 1 ga watan Janairun 2024, shugaban babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG Shen Haixiong, ya gabatar da jawabin murnar sabuwar shekara ga masu bibiyar CMG ta kafar talabijin ta CGTN, da gidan radiyon kasar Sin CRI da kuma kafar yanar gizo.

‘Yan uwa da abokai,
A yayin da hasken farko na ranar sabuwar shekara ya bayyana, mun sanya kafa cikin shekarar 2024 cike da fatan nasara. Ina gabatar muku gaisuwa ta daga nan birnin Beijing!

  • Shugabannin Sin Da Rasha Sun Tura Wa Juna Sakwanni Don Murnar Sabuwar Shekara
  • Sin Ta Mai Da Hankali Ga Kimiyya Da Fasaha

A shekarar 2023, shawarar “Ziri daya da hanya daya” ko BRI, ta cika shekaru 10 cikin karsashi, kasar Sin da duniya baki daya na samun ci gaba tare. A wannan hanya ta neman wadata, CMG ta ci gaba da yayata musaya tsakanin mabambantan wayewar kai, tare da cimma nasarori masu tarin yawa, ta hanyar shiga a dama da ita a harkokin duniya daban-daban.

A bana, mun sake daga matsayin kirkire-kirkire karkashin manufar “Tunani + Nuna Basira + Fasahohi” zuwa wani sabon mataki. Mun watsa shiri mai lakabin “Kalaman Magabata Na Xi Jinping (Zango na 2)” cikin harsuna da dama a kasashe sama da 80. Mun watsa shirye shiryen raya al’adu da dama masu wakiltar wayewar kan kasar Sin da sauran sassan duniya. Yawan wadanda suka kalli shirye-shiryen gasar wasannin motsa jiki na kasashen Asiya ta Hangzhou ta shafuka daban daban na yanar gizo, ya kai biliyan 41.4 wanda hakan ya kai matsayin koli a tarihi.

A bana, hadin gwiwar mu ta haifar da kyakkyawan sakamako. Tsoffin abokan mu sun zo haka ma sabbin abokan hulda. Mun sanya hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwa har 58 tare da kafofin CMG shirye-shirye na kasa da kasa, kana mun gudanar da karo na biyu na taron kirkire-kirkire a fannin ayyukan kafofin watsa labarai, da taron hadin gwiwar kafofin watsa labarai na kungiyar kasashen ASEAN, da taron hadin gwiwar kafofin watsa labarai na kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Karkashin ayyuka 51 na “Zamanantar da Sin da duniya “, da kuma bikin baje koli 8 na “Tafiya a tafarkin wayewar kai” wanda aka yi a sassan kasa da kasa, mun yi aiki tare da abokai na sassan duniya daban daban, inda muka bayyana kyakkyawar surar zamanantar da duniya bisa tafarkin ci gaba cikin lumana, da hadin gwiwar cimma moriya tare, da samar da wadatar bai daya.

Duniya a yau na fama da tashe-tashen hankula. Akwai matukar bukatar zaman lafiya, da ci gaba, da hadin gwiwa da cimma sakamako. Muna farin cikin ganin karin abokai na kasa da kasa na nuna fahimta, da lura tare da goyon bayan ra’ayoyi da mahangar kasar Sin.

A gefen taron APEC, mun gudanar da taron tattaunawa da mu’amalar al’adu a tsakanin Sin da Amurka a birnin San Francisco na Amurka, wanda ya samu kyakkyawar maraba. Mr. Harry Moyer, dattijon da ya kai shekaru 100, kuma mamba a kungiyar kawance ta “Flying Tigers”, ya kasance cikin wadanda suka halarci taron. Ya kuma shaida min cewa mahangar shugaba Xi game da gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, ta karbu a zukatan dukkanin al’umma. Bayan dawowa gida, na samu sakon kati, da kwallon taswirar duniya, da wasu kayan kawa da wasu yaran makarantar midil ta Lincoln dake Amurka suka aiko min. Kalli irin wannan kyauta, na yi farin ciki da tunanin yaran na zaman lafiya, da kauna, da kayatarwa da musaya tare da mu.

A matsayin ta na babbar kafar watsa labarai ta duniya ta fuskar girma da fadin sassa, CMG ta cika shekaru 5 da kafuwa, tana kuma kara karfi sannu a hankali. A bara, mun kammala bude reshensa na 191 a ketare, tare da kafa tsarin watsa shirye shirye dake hade kasashe da yankunan duniya 67. Kaza lika a karon farko, adadin masu kallo kafar CGTN a kasashen duniya sun haura miliyan 700. Kafar CGTN ta sha zama ta farko a duniya a fannin samar da labarai masu dumi-dumi game da manyan batutuwan kasa da kasa. Game da tafarkin gina sabon salon kafar watsa labarai mai karfi a duniya, za mu ci gaba da gaggauta aiwatar da burin mu na “gabatar da shirye-shirye masu inganci”.
Abokai, shekarar 2024 shekara ce ta dabbar “Loong” bisa kalandar gargajiyar kasar Sin.

Dabbar “Loong” ta kunshi tatsuniya game da wayewar kan kasar Sin, wanda ke wakiltar ruhin koyi daga kowa da kowa, da haifar da gajiya ga komai, da cimma matsaya guda yayin da ake kiyaye banbance banbance, da zama tare cikin jituwa.

Al’ummar Sinawa, ta ci gaba kan sabon tafarki, yayin da take bikin cika shekaru 75 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a wannan shekara ta “Loong”. CMG zai ci gaba da gabatar da labarai game da kasar Sin da ma duniya ga dukkanin bil Adama, zai ci gaba da rubuta sabbin babuka game da wayewar kan bil Adama, tare da yin maraba da sabuwar bazara!

Ina yiwa daukkanin al’ummar duniya fatan alheri a wannan sabuwar shekara! (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Xi

Xi Da Biden Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 45 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.