Shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Zamafara, Ahmad Sani Kaura, ya rasu yau Laraba a garin Gusau, babban birnin jihar.
An ruwaito cewa, marigayi Kaura, ya rasu ne bayan ya yanke jiki ya fadi a yayin wani taro na rattaba hannun yarjeniyar zaman lafiya da cibiyar malamai ta Ulama, reshen jihar da ta shirya don a gudanar da zaben 2023 ba tare da aukuwar wani hargitsin zabe ba.
- PDP Ta Maka APC A Kotu, Ta Nemi A Kori Shugaban APC Na Kasa Daga Mukaminsa
- Tsohon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Kano Pillars, Kofarmata, Ya Rasu
An ruwaito wani jigo a jam’iyyar PDP a Jihar Zamafara, Aminu Umar ya sanar cewa, marigayin ya kasance baya jin dadin jikinsa domin bai dade da warkewa daga jinya ba, amma ya halarci taron.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp