• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Sakandare Daga Zamfara Ya Zama Gwarzon Malami Na 2024 A Duk Faɗin Nijeriya 

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Wani shugaban makaranta daga jihar Zamfara ya zo na ɗaya a duk faɗin ƙasar nan a wajen bikin karrama Malamai na Shugaban ƙasa na shekarar 2024.

 

Ranar 5 ga watan Oktobar kowace shekara, rana ce da Ƙungiyar UNESCO ta ware don bikin ranar Malamai ta Duniya, wacce aka fara a shekarar 1994, ranar da aka ware don nuna jinjina, yabo da kuma nuna muhimmanci Malamai wajen ƙara kyautata rayuwar al’umma.

  • Gwamnatin Katsina Ta Sha Alwashin Kare Iyakokin Burtali A Jihar
  • Yadda Rayuwa Take A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Nijeriya

Sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume ne ya miƙa kyautar karramawar ta bana, a wani bikin da ya gudana a filin wasa na Eagle Square da ke Abuja.

 

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Shugaban makarantar gwamnati ta Sambo Secondary School da ke Gusau ne ya zama zakara a duk faɗin ƙasar nan a rukunin manyan makarantun gwamnati na ƙasa, inda ya lashe kyautar ta shugaban ƙasa.

 

An gwangwanje wannan Shugaban makaranta, Mallam Musa Yahaya Paila da wata dalleliyar mota da kuma lambar yabo.

Zamfara
Ya samu kyautar mota daga Shugaban Kasa

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa wannan mataki na yin nuni da cewa dokar ta-ɓacin da aka sanya wa harkar ilimi a Zamfara a ranar 14 ga watan Satumbar 2023 ya haifar ɗa mai ido.

 

Gwamnatin Dauda Lawal na cika alƙawarin ta na yi wa harkar ilimi garambawul, wanda gwamnatin ta tarar yana gab sa rushewa.”

 

Gwamnatin Nijeriya ta gabatar da bikin Malamai na duniya na bana 2024, mai taken “Muhimmantar da Muryoyin Malamai: Hanyar zuwa sabon yanayi ga harkar ilimi.”

 

A bikin, an karrama Malamai da shugabannin makarantu, tare da ba da kyaututtuka na musamman.

Zamfara

An zaƙulo waɗanda suka amfana ɗin ne daga makaramtun Sakandare da Firamare na gwamnati a duk faɗin ƙasar nan, da kuma makarantu masu zaman kan su, inda suka samu kyaututtukan da suka haɗa da motoci, babura, jannaretoci da sauran su.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Yadda Halin Yunwa Ke Jefa Mata Zinace-zinace

Yadda Halin Yunwa Ke Jefa Mata Zinace-zinace

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.