• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Syria

Daga ranar 21 zuwa 26 ga watan Satumba ne, shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya halarci bikin bude gasar wasannin motsa jiki ta Asiya dake gudana a birnin Hangzhou na kasar Sin. Wannan ita ce ziyara ta biyu da shugaba Bashar ya kawo Sin, tun bayan kusan shekaru 20.

A yayin wata zantawa da ya yi cikin shirin tattaunawa da shugabanni, na babban rukunin gidan rediyo da talabijin na kasar Sin(CMG), ya ce, kasar Sin ta samu ci gaba cikin sauri. A da ana kiran kasar Sin da “masana’antar duniya” ko kuma “masana’antar kayayyaki ta duniya,” amma yanzu muna iya cewa, kasar Sin ita ce “masana’antar kirkire-kirkire ta duniya”.

  • Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska
  • Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Binciken Duniyar Wata Mai Zuwa A Tsakanin Shekarar 2024

Shugaba Bashar ya jaddada cewa, ko da yake ci gaba da sauye-sauye na da matukar muhimmanci, amma yadda kasar Sin ta ke martaba ka’idoji daya shi ne ya fi muhimmanci. “Ko da ya ke ci gaba da sauye-sauye na iya haifar da wasu illoli, al’adun kasar Sin ba su sauya ba, kuma an san jama’ar kasar Sin da himma ga kasa, da al’umma, kuma al’adu ba su canza ba, wannan ita ce babbar nasara.”

A wannan bazarar, yankin Gabas ta Tsakiya ya samu “guguwar sulhu”. Baya ga komawar Syria cikin kungiyar kasashen Larabawa, bisa shiga tsakani na kasar Sin, kasashen Saudiyya da Iran sun sanar da dawo da huldar jakadanci a tsakaninsu. Dangane da wannan batu, shugaba Bashar ya bayyana cewa, an shafe sama da shekaru 40 ana rikici tsakanin kasashen Saudiyya da Iran a yankin, hakan ya faru ne sakamakon tsarin diflomasiyya na kasashen yamma, musamman salon diflomasiyyar kasar Amurka.

Kasar Amurka na haifar da matsaloli a tsakanin kasashe da dama, sannan ta kwace musu albarkatu domin amfanin kanta. Sanarwar da kasar Sin ta yi na yin sulhu tsakanin kasashen Saudiyya da Iran na nufin cewa, kasar Sin tana daukar matakai na zahiri, ba maganar fatar baki ko farfaganda kamar kasashen yammacin duniya ba, a maimakon haka, tana daukar matakai na siyasa na hakika da kuma samun sakamako.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

Shugaba Bashar ya kuma cewa, muna fatan kasar Sin za ta ci gaba da taka rawa a siyasance, kuma kamar yadda muka gani, za ta kara taka muhimmiyar rawa, wadda ke da alaka da kudurorin da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ciki har da shawarar samar da tsaro a duniya. Mun yi imanin cewa, wadannan tsare-tsare su ne ka’idodin sabuwar duniya.(Mai fassara: Ibrahim)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas
Daga Birnin Sin

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Next Post
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.