• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Afrika Za Su Sake Haduwa A Beijing Domin Tattauna Makomar Huldarsu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Sin Da Afrika Za Su Sake Haduwa A Beijing Domin Tattauna Makomar Huldarsu

A Shipping container is seen at the Lekki deep seaport before it was commission by Nigeria's President, Muhammadu Buhari, in Lagos, Nigeria, Monday, Jan. 23, 2023. Nigeria's President Muhammadu Buhari on Monday commissioned a Chinese-built and -funded $1.5 billion deep seaport in the commercial hub of Lagos with authorities optimistic the project would help grow the West African nation's ailing economy. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Alhamis, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kira wani taron manema labarai a gefen taro na 2 na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin karo na 14, inda ya amsa tambayoyin ’yan jarida game da manufofin Sin da dangantakarta da kasashen waje. 

Da aka tabo dangantakar Sin da Afrika, Wang Yi ya ce Sin da Afrika sun kasance ’yan uwan juna masu makoma ta bai daya. Kuma a matsayin babbar abokiyar huldar cinikayya ta nahiyar Afrika tsawon shekaru 15 a jere, nasarorin da huldar bangarorin biyu ta samu na kara habaka, lamarin dake kara kusancin zukatan al’ummominsu.

  • Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe
  • Li Qiang: Kamata Ya Yi Yunnan Ya Yi Amfani Da Fifikonsa Don Shiga Cikin Tsarin Rayawa Da Daidaita Harkoki Baki Daya Tsakanin Yankuna 

Yanzu haka, dangantakar kasashe masu tawo da Sin da Afrika ke wakilta, tana yin gagarumin tasiri ga tarihin duniya. Ya ce kasashen Afrika sun shiga wani sabon yanayi, inda suka gane cewa tsare-tsaren da aka kakaba musu daga waje, ba su haifar musu da kwanciyar hankali ko wadata ba. Ya ce akwai bukatar nahiyar Afrika ta lalubo hanyar da ta dace da yanayin kasashenta da kuma tsara makomarta da take so da kanta. A cewarsa a wannan sabon yanayin na tarihi, kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa da ’yan uwanta kasashen Afrika da mara wa nahiyar baya wajen tabbatar da ainihin ’yancinta, da taimaka mata inganta samun ci gaba bisa dogaro da kanta da kuma gaggauta tsarin zamanantar da nahiyar.

Wang Yi ya kara da cewa, a ko da yaushe, kasar Sin ta kasance mai adawa da nuna wariya ga nahiyar Afrika. Ya ce bayan irin dimbin ci gaba da dangantakar Sin da Afrika ta samu, yanzu wasu manyan kasashen duniya suna mayar da hankalinsu kan nahiyar Afrika, kuma Sin na maraba da hakan. Ya ce yana fatan dukkan bangarori, kamar Sin za su kara mayar da hankali kan nahiyar, da kara zuba mata jari da taimakawa ci gabanta. Haka kuma, suna maraba da shiga hadin gwiwa da karin kasashe bisa sharadin girmama dukkan bangarori.

A lokacin kaka na bana, za a gudanar da wani sabon taron koli na dandalin tattauna dangantakar Sin da Afrika a kasar Sin, inda shugabannin Sin da Afrika za su kara haduwa a Beijing bayan shekaru 6, domin tattauna makoma da tsare-tsaren ci gaban da na raya dangantakarsu da zurfafa musaya kan dabarun shugabanci. Game da hakan, ya ce ya yi imanin cewa, ta hanyar wannan taro, Sin da Afrika za su kara yaukaka dangantakarsu ta abota da zurfafa hadin kai da dangantaka da bude sabon babi na samun al’ummar nahiyar Afrika da Sin mai makoma ta bai daya. (Mai Fassarawa: Fa’iza Msutapha)

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe

Next Post

Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

15 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

16 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

17 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

18 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

19 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

20 hours ago
Next Post
Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika - MDD

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.