• English
  • Business News
Monday, May 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Afrika Za Su Sake Haduwa A Beijing Domin Tattauna Makomar Huldarsu

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Sin Da Afrika Za Su Sake Haduwa A Beijing Domin Tattauna Makomar Huldarsu

A Shipping container is seen at the Lekki deep seaport before it was commission by Nigeria's President, Muhammadu Buhari, in Lagos, Nigeria, Monday, Jan. 23, 2023. Nigeria's President Muhammadu Buhari on Monday commissioned a Chinese-built and -funded $1.5 billion deep seaport in the commercial hub of Lagos with authorities optimistic the project would help grow the West African nation's ailing economy. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Alhamis, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kira wani taron manema labarai a gefen taro na 2 na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin karo na 14, inda ya amsa tambayoyin ’yan jarida game da manufofin Sin da dangantakarta da kasashen waje. 

Da aka tabo dangantakar Sin da Afrika, Wang Yi ya ce Sin da Afrika sun kasance ’yan uwan juna masu makoma ta bai daya. Kuma a matsayin babbar abokiyar huldar cinikayya ta nahiyar Afrika tsawon shekaru 15 a jere, nasarorin da huldar bangarorin biyu ta samu na kara habaka, lamarin dake kara kusancin zukatan al’ummominsu.

  • Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe
  • Li Qiang: Kamata Ya Yi Yunnan Ya Yi Amfani Da Fifikonsa Don Shiga Cikin Tsarin Rayawa Da Daidaita Harkoki Baki Daya Tsakanin Yankuna 

Yanzu haka, dangantakar kasashe masu tawo da Sin da Afrika ke wakilta, tana yin gagarumin tasiri ga tarihin duniya. Ya ce kasashen Afrika sun shiga wani sabon yanayi, inda suka gane cewa tsare-tsaren da aka kakaba musu daga waje, ba su haifar musu da kwanciyar hankali ko wadata ba. Ya ce akwai bukatar nahiyar Afrika ta lalubo hanyar da ta dace da yanayin kasashenta da kuma tsara makomarta da take so da kanta. A cewarsa a wannan sabon yanayin na tarihi, kasar Sin za ta ci gaba da tsayawa da ’yan uwanta kasashen Afrika da mara wa nahiyar baya wajen tabbatar da ainihin ’yancinta, da taimaka mata inganta samun ci gaba bisa dogaro da kanta da kuma gaggauta tsarin zamanantar da nahiyar.

Wang Yi ya kara da cewa, a ko da yaushe, kasar Sin ta kasance mai adawa da nuna wariya ga nahiyar Afrika. Ya ce bayan irin dimbin ci gaba da dangantakar Sin da Afrika ta samu, yanzu wasu manyan kasashen duniya suna mayar da hankalinsu kan nahiyar Afrika, kuma Sin na maraba da hakan. Ya ce yana fatan dukkan bangarori, kamar Sin za su kara mayar da hankali kan nahiyar, da kara zuba mata jari da taimakawa ci gabanta. Haka kuma, suna maraba da shiga hadin gwiwa da karin kasashe bisa sharadin girmama dukkan bangarori.

A lokacin kaka na bana, za a gudanar da wani sabon taron koli na dandalin tattauna dangantakar Sin da Afrika a kasar Sin, inda shugabannin Sin da Afrika za su kara haduwa a Beijing bayan shekaru 6, domin tattauna makoma da tsare-tsaren ci gaban da na raya dangantakarsu da zurfafa musaya kan dabarun shugabanci. Game da hakan, ya ce ya yi imanin cewa, ta hanyar wannan taro, Sin da Afrika za su kara yaukaka dangantakarsu ta abota da zurfafa hadin kai da dangantaka da bude sabon babi na samun al’ummar nahiyar Afrika da Sin mai makoma ta bai daya. (Mai Fassarawa: Fa’iza Msutapha)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe

Next Post

Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

Related

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

2 hours ago
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

5 hours ago
Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 
Daga Birnin Sin

Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 

8 hours ago
An Ziyarci Gidajen Tarihin Kasar Sin Sau Biliyan 1.49 A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

An Ziyarci Gidajen Tarihin Kasar Sin Sau Biliyan 1.49 A Shekarar 2024

9 hours ago
Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 
Daga Birnin Sin

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

1 day ago
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

1 day ago
Next Post
Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika - MDD

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

May 18, 2025
Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?

May 18, 2025
Ciwon Mara Lokacin Al’ada

Ciwon Mara Lokacin Al’ada

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Bunkasar Masana’antar Harkokin Tauraron Dan Adam A Shekarar 2024

May 18, 2025
Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe

May 18, 2025
An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

An Cafke Mai Garkuwa Da Mutane A Sansanin Alhazan Abuja

May 18, 2025
Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

Kasar Sin Ta Sanya Harajin Takaita Shigo Da Kayayyakin Robobi Masu Tauri

May 18, 2025
Yadda Ake Hada Danderun Kaza

Yadda Ake Hada Danderun Kaza

May 18, 2025
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

May 18, 2025
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

May 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.