• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump, jiya Alhamis, bisa bukatar da Trump ya gabatar.

Xi Jinping ya ce, ya kamata kasashen biyu su zama jagorori, tare da kawar da matsalolin dake gabansu, domin daidaita dangantakarsu. Bisa rokon da Amurka ta gabatar, masu jagorantar tattaunawar harkokin tattalin arziki da cinikayya na kasashen biyu sun tattauna a birnin Geneva, inda suka taka rawa wajen warware sabanin dake tsakanin Sin da Amurka a fannin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar yin shawarwari, lamarin da ya samu amincewa daga bangarori daban daban na kasashen biyu, da ma gamayyar kasa da kasa. Hakan kuma ya nuna cewa, yin shawarwari da hadin gwiwa, ita ce hanya kadai da ya kamata su bi.

Shugaba Xi ya kara da cewa, ya kamata Sin da Amurka su yi amfani da tsarin yin shawarwari kan harkokin tattalin arziki da ciniki da suka kafa da kansu yadda ya kamata, tare da tabbatar da adalci, da girmama matsayar juna, domin cimma moriyar juna. Ya ce kasar Sin tana son bin wannan tsarin, a sa’i daya kuma, tana da ka’idojinta na kanta. A cewar shugaba Xi, idan Sinawa suka yi alkawari, tabbas za su cika.

A halin yanzu, Sin da Amurka sun cimma ra’ayi daya, don haka ya zama dole bangarorin biyu su bi wannan ra’ayi daya da suka cimma.

Bayan tattaunawar da aka yi a birnin Geneva, kasar Sin ta yi aiki bisa yarjejeniyar, don haka ya kamata kasar Amurka ta duba sakamakon da aka samu da idon basira, kuma ta soke matakan da ba su dace ba. Haka kuma, zai fi kyau Sin da Amurka su karfafa mu’amalar dake tsakaninsu kan harkokin diflomasiyya, da tattalin arziki da ciniki, da aikin soja da dai sauransu, domin kara fahimtar juna, da warware sabanin dake tsakaninsu, tare da kuma zurfafa hadin gwiwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Bugu da kari, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata kasar Amurka ta daidaita matsayinta kan batun Taiwan da idon basira, kada masu neman raba yankin Taiwan daga kasar Sin su tura Amurka da Sin cikin rikici.

A nasa bangare, shugaba Trump na Amurka ya ce, yana matukar girmama shugaba Xi Jinping, kuma huldar dake tsakanin Amurka da Sin tana da muhimmanci. Ya ce kasar Amurka ta yi farin cikin ganin karuwar tattalin arzikin kasar Sin. Kana, hadin gwiwar dake tsakanin Amurka da Sin za ta ba da gudummawa ga kasa da kasa. Ya ce a nan gaba kuma, kasarsa za ta ci gaba da bin manufar kasar Sin kasa daya tak a duniya. Bugu da kari, ya ce kasashen biyu sun samu nasarar tattaunawar tattalin arizki da cinikayya a birnin Geneva, inda suka kuma cimma kyakkyawar yarjejeniyar. Kasar Amurka tana fatan hadin gwiwa da kasar Sin wajen aiwatar da yarjejeniyar, haka kuma tana maraba da zuwan daliban kasar Sin.

Kaza lika, shugaba Xi ya yi maraba da Donald Trump ya sake kawowa kasar Sin ziyara, inda shi kuma shugaba Trump ya bayyana godiyarsa matuka. Daga bisani, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan ci gaba da aiwatar da ra’ayi daya da aka cimma a birnin Geneva, yayin gudanar da sabon zagayen taron tattaunawa. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Next Post

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Related

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

3 hours ago
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

4 hours ago
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

5 hours ago
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

7 hours ago
An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
Daga Birnin Sin

An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 

8 hours ago
Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Yawan Tallafinta Ga Hukumar Kula Da ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinu

9 hours ago
Next Post
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

LABARAI MASU NASABA

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.