• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Uganda Na Sa Ran Karfafa Hadin Gwiwarsu A Fannin Gina Ababen More Rayuwa Ga Kirkire-Kirkire

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Jiya Alhamis ne aka gudanar da taron murnar cika shekaru 60, da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin kasar Sin da kasar Uganda ta kafar bidiyo.

A yayin taron, mataimakin shugaban kungiyar sada zumunci da kasashen waje ta kasar Sin Jiang Jiang, ya bayyana cewa, a halin yanzu, ya kamata kasar Sin da kasashen Afirka su hada kansu, wajen karfafa hadin gwiwa a fannonin gina ababen more rayuwa, da gudanar da kirkire-kirkire ta fuskar harkokin sadarwa, da neman bunkasuwa ta hanyar kare muhalli, domin neman babban ci gaba.

  • ’Yan Sama Jannati Na Kasar Sin Sun Gayyaci Matasan Duniya Da Su Ziyarci Tashar Sararin Samaniyar Sin

A nata bangare, jakadar kasar Uganda dake kasar Sin Oliver Wonekha ta bayyana cewa, shekarar 2022 wata muhimmiyar shekara ce, domin a cikin ta ake cika shekaru 60 da kafuwar huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Uganda da kasar Sin, kuma cikin wadannan shekaru da suka gabata, ana ci gaba da zurfafa dangantakar abokantaka a tsakanin kasashen biyu, yayin da aka cimma sakamako da dama.

Tana mai cewa, “Kasar Sin ta kasance daya daga cikin kasashen da suka fi zuba jari a kasar Uganda, wanda hakan ta taka muhimmiyar rawa a fannin raya tattalin arzikin kasar Uganda, shi ya sa, gwamnatin kasar take godiya matuka dangane da taimakon da kasar Sin ta samar mata.

Kaza lika kasar Sin ta samar da taimakon kudi ga wasu muhimman shirye-shiryen raya kasar Uganda, kamar na gina tashar samar da wutar lantarki da karfin ruwa ta Karuma, da gina manyan hanyoyin mota tsakanin birnin Entebbe da birnin Kampala da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Kuma, bisa bayanin da aka fidda, ya zuwa shekarar 2020, karfin cinikayya a tsakanin kasashen biyu, ya zarce dallar Amurka har biliyan 1.

Kasar Sin ta kuma ba da gudummawa matuka ga kasar Uganda, a fannin gudanar da kwaskwarima, da neman ci gaba, bisa tsarin dandalin tattauna hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka wato FOCAC”. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Farmaki Hadimin Gwamnan Bauchi, Sun Jikkata Mutum 1

'Yan Bindiga Sun Farmaki Hadimin Gwamnan Bauchi, Sun Jikkata Mutum 1

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.