• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a taron manema labaru da aka saba gudanarwa a yau Alhamis ranar 11 ga wata cewa, sanarwar taron koli na Washington na kungiyar tsaro ta NATO ta yi karin gishiri kan halin da ake ciki a yankin Asiya da tekun Pasifik, kuma tana cike da tunanin yakin cacar-baka da kalamai masu iya tayar da yaki, kana abubuwan da sanarwar ta alakanta da kasar Sin suna cike da son zuciya, batanci da tsokana, wadanda ba mu yarda da su ba kuma mun nuna matukar takaici game da haka ga NATO.

Kaza lika, jami’in ya nuna cewa, an gudanar da wannan taro ne a daidai lokacin da kungiyar tsaro ta NATO ta cika shekaru 75 da kafuwa, domin nuna wajabcin wanzuwarta, kasar Amurka da NATO sun mayar da ita a matsayin “kungiyar wanzar da zaman lafiya” kafin taron, amma ba za a taba boye gaskiya cewa ta zama tarihi sakamakon yakin cacar baka, da rura wutar adawa da kuma kafa kananan kungiyoyin siyasa da take yi ba.

  • Tsaro Da NATO Take Magana Ya Dagora Ne Kan Salwantar Tsaron Sauran Mutane
  • Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Kan Yadda Take Kiyaye Muhallin Halittun Teku

An ba da rahoton cewa, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana a gun dandalin tattaunawa na taron koli na kungiyar tsaro ta NATO a jiya Laraba cewa, a cikin shekara daya da rabi da ya gabata, mun ga yadda kasar Rasha ta samu karin makamai, wanda ya samo asali ne daga taimakon da kasar Sin ke bayarwa ga tushen harkokin tsaron kasar ta Rasha.

Game da wannan batu, Lin Jian ya bayyana cewa, kasar Sin tana kakkausar adawa da ci gaba da yada labaran karya da Amurka ke yi, na cewa kasar Sin tana goyon bayan masana’antun tsaron kasa na Rasha ba tare da wata shaida ba.

Lin Jian ya sake nanata cewa, maimakon nuna goyon baya ga wani bangare a cikin rikice-rikice, kamata ya yi Amurka ta yi tunani kan musabbabin rikicin, ta kuma yi wani abu mai amfani don tabbatar da zaman lafiya da gaske. (Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Da TUC Za Su Sake Sabon Zama Da Tinubu A Mako Mai Zuwa

Next Post

Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

6 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

9 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.