• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a taron manema labaru da aka saba gudanarwa a yau Alhamis ranar 11 ga wata cewa, sanarwar taron koli na Washington na kungiyar tsaro ta NATO ta yi karin gishiri kan halin da ake ciki a yankin Asiya da tekun Pasifik, kuma tana cike da tunanin yakin cacar-baka da kalamai masu iya tayar da yaki, kana abubuwan da sanarwar ta alakanta da kasar Sin suna cike da son zuciya, batanci da tsokana, wadanda ba mu yarda da su ba kuma mun nuna matukar takaici game da haka ga NATO.

Kaza lika, jami’in ya nuna cewa, an gudanar da wannan taro ne a daidai lokacin da kungiyar tsaro ta NATO ta cika shekaru 75 da kafuwa, domin nuna wajabcin wanzuwarta, kasar Amurka da NATO sun mayar da ita a matsayin “kungiyar wanzar da zaman lafiya” kafin taron, amma ba za a taba boye gaskiya cewa ta zama tarihi sakamakon yakin cacar baka, da rura wutar adawa da kuma kafa kananan kungiyoyin siyasa da take yi ba.

  • Tsaro Da NATO Take Magana Ya Dagora Ne Kan Salwantar Tsaron Sauran Mutane
  • Sin Ta Gabatar Da Takardar Bayani Kan Yadda Take Kiyaye Muhallin Halittun Teku

An ba da rahoton cewa, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya bayyana a gun dandalin tattaunawa na taron koli na kungiyar tsaro ta NATO a jiya Laraba cewa, a cikin shekara daya da rabi da ya gabata, mun ga yadda kasar Rasha ta samu karin makamai, wanda ya samo asali ne daga taimakon da kasar Sin ke bayarwa ga tushen harkokin tsaron kasar ta Rasha.

Game da wannan batu, Lin Jian ya bayyana cewa, kasar Sin tana kakkausar adawa da ci gaba da yada labaran karya da Amurka ke yi, na cewa kasar Sin tana goyon bayan masana’antun tsaron kasa na Rasha ba tare da wata shaida ba.

Lin Jian ya sake nanata cewa, maimakon nuna goyon baya ga wani bangare a cikin rikice-rikice, kamata ya yi Amurka ta yi tunani kan musabbabin rikicin, ta kuma yi wani abu mai amfani don tabbatar da zaman lafiya da gaske. (Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Da TUC Za Su Sake Sabon Zama Da Tinubu A Mako Mai Zuwa

Next Post

Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

Related

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

7 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

7 hours ago
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

9 hours ago
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

10 hours ago
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

12 hours ago
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

12 hours ago
Next Post
Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.