• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

Yau Alhamis, an fara jigilar kayayyakin aikin jinya da za su biya bukatun mutane 5000 daga birnin Beijing na kasar Sin zuwa kasar Syria, wadanda suka kasance agajin jerin farko da kungiyar ba da agaji ta Red Cross ta kasar Sin ta samar wa yankunan kasar Syria, wadanda bala’in girgizar kasa ya ritsa da su.

Bayan barkewar mummunar girgizar kasa a kasashen Turkiye da Syria, a ranar Litinin da ta gabata, kungiyar Red Cross ta kasar Sin ta fara daukar matakai ba tare da wani jinkiri ba. Ta riga ta ba kungiyoyin Red Crescent na kasashen 2 tallafin kudi, inda kowaccensu ta samu dalar Amurka dubu 200. Haka zalika, kungiyar na ci gaba da lura da bukatun da ake samu a yankunan kasashen da Iftila’in ya ritsa da su, tare da samar da dauki gwargwadon karfinta.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta gabatar da yadda kasarta take kokarin samar da tallafi ga kasashen Turkiyya da Siriya da iftila’in girgizar kasa mai karfin gaske ya shafa, inda ta ce, baya ga kudade da tallafin kaya, kasar na gaggauta aikin samar da tallafin abinci ga Siriya, ciki har da alkama ton 220 dake kan hanya, da kuma shinkafa da alkama sama da ton 3000 da za’a yi jigilarsu nan bada jimawa ba.

Mao ta ce, jim kadan bayan isarsu Turkiyya, ma’aikatan ceto na kasar Sin suka fara ayyukan ceto a birnin Antakya na jihar Hatay il inda bala’in ya fi yi wa muni, kuma bisa hadin-gwiwa da takwarorin su na kasar Turkiyya, sun ceto wata mata mai juna biyu daga baraguzan wani gini da sanyin safiyar yau Alhamis. Kana, da daren jiya Laraba, gwamnatin yankin Hong Kong na kasar Sin ita ma ta tura wata kungiya mai ma’aikatan ceto 59 zuwa Turkiyya don samar da taimako. Har ila yau, da safiyar yau Alhamis, an soma jigilar kayayyakin aikin jinya da za su biya bukatun mutane 5000 daga birnin Beijing na kasar Sin zuwa kasar Siriya, wadanda suka kasance agaji jerin farko da kungiyar bada agaji ta Red Cross ta kasar Sin ta samar wa yankunan kasar Siriya, wadanda bala’in girgizar kasa ya ritsa da su. Ma’aikatan ceto na kungiyar Red Cross ta kasar Sin su ma sun tafi Siriya. (Bello Wang, Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Next Post

2023: Kashi 90 Na Shirye-Shiryen Zabe Ya Kammala – INEC

Related

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

13 hours ago
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
Daga Birnin Sin

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

14 hours ago
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu
Daga Birnin Sin

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

16 hours ago
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

18 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

18 hours ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

2 days ago
Next Post
2023: Kashi 90 Na Shirye-Shiryen Zabe Ya Kammala – INEC

2023: Kashi 90 Na Shirye-Shiryen Zabe Ya Kammala - INEC

LABARAI MASU NASABA

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.