• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Bayyana Adawa Da Karin Kasafin Kudaden Ayyukan Soji Na Wasu Kasashe Karkashin Manufar “Barazanar Ayyukan Sojin Kasar”

byCMG Hausa
3 years ago
Sin

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Tan Kefei, ya bayyana matukar adawar kasar Sin, da yadda wasu kasashe suka kara adadin kudaden da suke kashewa a fannin ayyukan soji, karkashin manufar da suka kira “Dakile barazanar ayyukan sojin kasar Sin”. 

Tan Kefei, ya ce har kullum Sin na aiwatar da manufofi ne na wanzar da zaman lafiya, wanda hakan ke taimakawa matuka wajen tabbatar da doka da oda a duniya baki daya. Kaza lika ga ragowar sassan duniya, Sin ta zama ginshikin samar da damammaki ba wai kalubale ba.

  • Li Qiang: Kwarin Gwiwar Da Kasar Sin Ke Da Shi Ya Kasance Jigo Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaba A Duniya

Jami’in ya kara da cewa, Amurka ta kasance a sahun gaba tsakanin kasashen duniya, a fannin yawan kasafin kudin ayyukan soji, a hannu guda kuma, ita ce kasar dake ingiza yake-yake da haifar da rudani. Har ila yau, Amurka ce babbar barazana ga zaman lafiyar duniya, da tsaro da daidaito. A sa’i daya kuma, Sin na kira ga Birtaniya da ta rungumi halayya ta gari, ta yi wa kasar Sin kyakkyawar fahimta, ta kuma dakatar da yayata zargin da ake yi wa kasar Sin, na kasancewa barazana ga saura.

Game da batun hadin gwiwar da Amurka da Birtaniya da Australia ke yi wajen kirar jirgin karkashin ruwa mai amfani da makamashin nukiliya kuwa, Tan ya ce Sin na matukar adawa da wannan hadin gwiwa da kasashen 3 suka kira da “Hadin kai a fannin tsaro”.

Ya ce, irin wannan karamar gamayya da aka gina kan tunani irin na cacar baka, ba za ta haifarwa kowa da mai ido ba. A nata bangare kuwa, Sin na fatan kasashen da batun ya shafa za su lura da salon ci gaba na wannan zamani, su yi watsi da son kai don cimma moriyar su, su kuma saurari kiraye-kirayen sassan kasa da kasa da budaddiyar zuciya, kana su sauke nauyin dake wuyan su na cudanyar kasa da kasa, tare da ba da karin gudummawa wajen wanzar da zaman lafiya, da daidaito a dukkanin shiyyoyi. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Yanzu-Yanzu: Mataimakin Zababben Shugaban Kasa, Shettima Ya Gana Da IBB

Yanzu-Yanzu: Mataimakin Zababben Shugaban Kasa, Shettima Ya Gana Da IBB

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version