A jiya ne, kasar Sin ta yi kira ga daukacin kasashen duniya da su hada kai, wajen yin kira ga kasar Japan da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya daga tashar nukiliyar Fukushima Daiichi zuwa cikin teku.
Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya shaidawa babban zauren MDD cewa, wajibi ne a kaucewa haifar da illa da hadari ga muhallin teku na duniya da lafiya da jin dadin al’ummar duniya.(Ibrahim)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp