• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Nuna Bakin Ciki Kan Mutuwar Fararen Hula A Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
Isra'ila

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin ta yi matukar bakin ciki kan yadda fararen hula suka rasa rayukansu, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kuma tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

Mao ta bayyana hakan ne yau Litinin din nan a yayin taron manema labarai na yau da kullum don yin karin haske kan rikicin dake faruwa a tsakanin Isra’ila da kungiyoyin Falasdinawa masu dauke da makamai a yankin zirin Gaza, wanda ya janyo hasarar dimbin rayuka a tsakanin bangarorin biyu.

  • Xi Ya Fadawa Schumer Yadda Sin Da Amurka Za Su Daidaita Zai Tabbatar Da Makomar Bil Adama
  • ‘Yan Jarida Sun Yaba Da Ci Gaba Da Al’adun Jihar Xinjiang

Mao ta ce, kasar Sin ta damu matuka game da yadda rikicin Palasdinu da Isra’ila ke ci gaba da rincabewa a baya-bayan nan, kuma ta yi matukar bakin ciki da hasarar rayukan fararen hula da rikicin ya haifar. Tana mai cewa, kasar Sin tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

A cewarta, kasar Sin na adawa da ayyukan da ke kara ta’azzara rikicin da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar yankin, tana kuma fatan ganin an tsagaita bude wuta da dawo da zaman lafiya nan da nan. Ta ce, ya kamata kasashen duniya su taka rawar da ta dace da kuma hada kai, don yayyafawa lamarin ruwa.

Sannan, a jiya Lahadi ne kwamitin tsaron MDD ya gudanar da zaman gaggawa na sirri, bayan da dakarun Falasdinawa suka kaddamar da muggan hare-hare kan yankunan Isra’ila dake zirin Gaza.

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Cikin tsokacin da ya yi game da hakan, wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya yi kira ga sassan da rikicin ya shafa da su kai zuciya nesa, tare da kaucewa rura wutar rikicin.

Zhang ya kara da cewa, Sin ta yi matukar damuwa bisa dauki ba dadin da ya barke tsakanin sojojin Isra’ila da dakarun Falasdinu a Gaza, wanda hakan ya sabbaba rasuwar fararen hula masu yawa. Ya ce Sin ta damu da yiwuwar kara kazantar fadan.

Daga nan sai jami’in ya jaddada kira ga dukkanin sassan da rikicin ya shafa, da su dakile ta’azzarar fadan, su kuma amincewa matakan tsagaita bude wuta. Kaza lika su rungumi matakan ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kai ba tare da wani bata lokaci ba.

Da yammacin jiya Lahadi, kafofin watsa labaran Isra’ila da dama sun bayyana cewa, sabon fada ya kara rincabewa tsakanin sassan biyu, wanda hakan ya haifar da kisan al’ummar Isra’ila sama da 700.

A daya bangaren kuma, hukumar kiwon lafiya ta Falasdinawa dake zirin Gaza, ta fitar da sanarwa a daren jiyan, wadda a ciki ta bayyana cewa, harin sojojin Isra’ila a zirin na Gaza, ya hallaka a kalla mutane 413 tare da jikkata wasu 2300. (Masu Fassarawa: Ibrahim Yaya, Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Daga Birnin Sin

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Next Post
Kisa

Kotu Ta Yanke Wa Jami'in 'Yansandan Da Ya Harbe Lauya Raheem Hukuncin Kisa A Legas

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.