• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Nuna Bakin Ciki Kan Mutuwar Fararen Hula A Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Isra'ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin ta yi matukar bakin ciki kan yadda fararen hula suka rasa rayukansu, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kuma tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

Mao ta bayyana hakan ne yau Litinin din nan a yayin taron manema labarai na yau da kullum don yin karin haske kan rikicin dake faruwa a tsakanin Isra’ila da kungiyoyin Falasdinawa masu dauke da makamai a yankin zirin Gaza, wanda ya janyo hasarar dimbin rayuka a tsakanin bangarorin biyu.

  • Xi Ya Fadawa Schumer Yadda Sin Da Amurka Za Su Daidaita Zai Tabbatar Da Makomar Bil Adama
  • ‘Yan Jarida Sun Yaba Da Ci Gaba Da Al’adun Jihar Xinjiang

Mao ta ce, kasar Sin ta damu matuka game da yadda rikicin Palasdinu da Isra’ila ke ci gaba da rincabewa a baya-bayan nan, kuma ta yi matukar bakin ciki da hasarar rayukan fararen hula da rikicin ya haifar. Tana mai cewa, kasar Sin tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

A cewarta, kasar Sin na adawa da ayyukan da ke kara ta’azzara rikicin da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar yankin, tana kuma fatan ganin an tsagaita bude wuta da dawo da zaman lafiya nan da nan. Ta ce, ya kamata kasashen duniya su taka rawar da ta dace da kuma hada kai, don yayyafawa lamarin ruwa.

Sannan, a jiya Lahadi ne kwamitin tsaron MDD ya gudanar da zaman gaggawa na sirri, bayan da dakarun Falasdinawa suka kaddamar da muggan hare-hare kan yankunan Isra’ila dake zirin Gaza.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Cikin tsokacin da ya yi game da hakan, wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya yi kira ga sassan da rikicin ya shafa da su kai zuciya nesa, tare da kaucewa rura wutar rikicin.

Zhang ya kara da cewa, Sin ta yi matukar damuwa bisa dauki ba dadin da ya barke tsakanin sojojin Isra’ila da dakarun Falasdinu a Gaza, wanda hakan ya sabbaba rasuwar fararen hula masu yawa. Ya ce Sin ta damu da yiwuwar kara kazantar fadan.

Daga nan sai jami’in ya jaddada kira ga dukkanin sassan da rikicin ya shafa, da su dakile ta’azzarar fadan, su kuma amincewa matakan tsagaita bude wuta. Kaza lika su rungumi matakan ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kai ba tare da wani bata lokaci ba.

Da yammacin jiya Lahadi, kafofin watsa labaran Isra’ila da dama sun bayyana cewa, sabon fada ya kara rincabewa tsakanin sassan biyu, wanda hakan ya haifar da kisan al’ummar Isra’ila sama da 700.

A daya bangaren kuma, hukumar kiwon lafiya ta Falasdinawa dake zirin Gaza, ta fitar da sanarwa a daren jiyan, wadda a ciki ta bayyana cewa, harin sojojin Isra’ila a zirin na Gaza, ya hallaka a kalla mutane 413 tare da jikkata wasu 2300. (Masu Fassarawa: Ibrahim Yaya, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuHamasIsra'ilawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Fadawa Schumer Yadda Sin Da Amurka Za Su Daidaita Zai Tabbatar Da Makomar Bil Adama

Next Post

Kotu Ta Yanke Wa Jami’in ‘Yansandan Da Ya Harbe Lauya Raheem Hukuncin Kisa A Legas

Related

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

28 minutes ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

1 hour ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

2 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

3 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

4 hours ago
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 
Daga Birnin Sin

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

5 hours ago
Next Post
Kisa

Kotu Ta Yanke Wa Jami'in 'Yansandan Da Ya Harbe Lauya Raheem Hukuncin Kisa A Legas

LABARAI MASU NASABA

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.