• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Tsara Kyawawan Sharuddan Janyo Jarin Waje

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Tsara Kyawawan Sharuddan Janyo Jarin Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jita-jita da wasu ke yadawa wai, masu jarin wajen na janyewa daga kasar Sin ko kadan ba gaskiya ba ne.

Idan ba a manta ba, a kwanakin baya majalisar gudanarwar Sin ta fitar wasu dokoki da suka shafi yadda za a kara jawo jarin waje da ma cin gajiyarsa yadda ya kamata. Dokokin sun bukaci da a inganta yanayin da ake ciki a cikin gida da waje, da bunkasa yanayin kasuwar da babu kamarta a duniya, wanda kuma za ta dace da yanayi na kasuwaci, bisa doka da ka’idoji na kasa da kasa.

  • Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kaucewa Aiwatar Da Matakan Da Ka Iya Barazana Ga Tsaronta

Ita ma hukumar dake tsara harkokin tattalin arzikin kasar Sin ta bayyana a yayin wani taro cewa, za ta himmatu wajen kara ci gaba da yin gyare-gyare, da nacewa kan ka’idar tabbatar da bunkasar tattalin arziki yadda ya kamata a matsayin babban fifiko, da neman ci gaba, yayin da ake tabbatar da daidaito.
A cewar taron, hukumar raya kasa da yin gyare-gyare, wadda ke tsara bunkasar tattalin arziki, ta bayyana ayyuka shida a wurin taron, wadanda suka hada da ka’idojin tafiyar da harkokin kudi, inganta amfani da kayayyaki da kara zuba jari, tallafawa ayyukan samar da kayayyaki da hidima, zurfafa gyare-gyare da bude kofa, karfafa ginshikin tsaron tattalin arziki, da tabbatar da kyautata jin dadin jama’a.

Bugu da kari taron ya bayyana cewa, tattalin arzikin kasar Sin yana da karfin juriya, da samar da damammaki, da kuzari, kuma tushen tattalin arzikin kasar na dogon lokaci bai canza ba.

Sanin kowa ne cewa, akwai dimbin damammaki na harkokin kasuwancin duniya a babbar kasuwar kasar Sin, da cikakken tsarin masana’antu, da sabbin hanyoyin bunkasuwa.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Alkaluma na nuna cewa, GDPn kowane mutum a kasar Sin, ya zarce dalar Amurka dubu 12, kuma rukunin masu matsakaicin kudin shiga, ya zarce miliyan 400, wanda ya samar da babbar kasuwar cikin gida mai dimbin damammaki. Kasar Sin ita ce kasa daya tilo da ke da dukkan nau’o’in masana’antu da MDD ta lissafa, kuma fa’idar da take da su a masana’antu, ba za a taba hada su da na sauran kasashe ba.

A makon da ya gabata ne kuma, aka gudanar da babban taron kolin raya tattalin arziki na shekara-shekara, don yanke shawarar ba da fifiko kan ayyukan raya tattalin arzikin kasar a shekarar 2024. Kuma a yayin taron, shugabannin kasar Sin sun yi alkawarin fadada bude kofa mai inganci ga kasashen waje. Don haka, yada karya game da janyewar jarin waje a kasar Sin, labarin kanzon kurege ne, wanda ba shi da wani tushe, balle madafa. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Idan Ana Maganar Kamfanonin Sin, Ita Kanta Burtaniya Ma Za Ta Ji Radadin

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Kasar Rasha

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

8 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

8 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

9 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

11 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

12 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

14 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Kasar Rasha

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Kasar Rasha

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.