Ma’aikatar kudi da ma’aikatar madatsar ruwa na kasar Sin sun bayyana a yau Laraba cewa, kasar Sin ta ware yuan biliyan 1, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 139.69, don daidaita asarar da aka yi a yankunan kogin Haihe da suka yi fama da bala’in ambaliyar ruwa a baya-bayan nan.
Za a yi amfani da kudin don biyan diyya ga asarar dukiyoyi na mazauna wadannan yankuna, da suka hada da lalacewar amfanin gona, filayen kiwon dabbobi da kaji, dazuzzuka na kasuwanci, gidaje da injunan noma, don taimaka musu fara aiki da rayuwa cikin gaggawa, in ji ma’aikatun. (Mai fassara: Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp