Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin Wang Wenbin, ya ce fashewar da ta lalata bututun iskar gas na Nord Stream, wanda babban muhimmin aiki ne na jigilar iskar gas, na da mummunan tasiri ga kasuwar makamashi ta duniya, da muhallin halittu, kuma hakan zai sanya kasashen duniya cikin damuwa, game da tsaron manyan ababen more rayuwa da ake da su.
Wang Wenbin, wanda ya bayyana hakan a Alhamis din nan, ya kara da cewa, ya zama wajibi a gudanar da bincike bisa adalci, da kwarewa, tare da hukunta wadanda suke da hannu cikin aikata wannan ta’asa. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp