• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Mahara 14, Sun Ceto Wadanda Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna Da Neja

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Sojoji Sun Kashe Mahara 14, Sun Ceto Wadanda Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna Da Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun runduna ta daya ta sojojin Nijeriya da ke Kaduna, a ci gaba da kokarin kawar da ‘yan ta’adda, sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda daga maboya da dama, inda suka kashe 14 daga cikinsu, tare da samun nasarar kwato manyan makamai da sauran kayayyaki a wasu hare-haren hadin gwiwa a jihohin Kaduna da Neja.

A cikin wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya, ya fitar kuma aka rabawa manema labarai, ta ce a jihar Neja a ranar 23 ga watan Disamba, 2023, sojojin sun kai hare-hare garin Madawaki da ke karamar hukumar Shiroro ta jihar inda suka kashe wasu mahara biyu sauran suka tsere da raunukan harbin bindiga.

  • Adadin Masu Fama Da Cututtukan Numfashi Dake Neman Jinya A Cibiyoyin Lafiya A Kasar Sin Na Raguwa
  • Hukuncin Kotu: INEC Ta Baiwa ‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Filato 16 Shaidar Lashe Zabe

Ya kara da cewa, sojojin sun kwato bindigogin AK47 guda biyu, kwalbasar alburusan AK47 guda biyu da babur daya.

“Sojoji sun zarce zuwa sansanin da aka kashe jagoran ‘yan bindiga, Ali Kachalla, inda ragowar ‘yan ta’addan suke, yayin da suka hango tawagar jami’an tsaron sai suka tsere suka bar mutanen da suka yi garkuwa da su a sansaninsu su 13, dukkansu maza ne, an sace su ne a jihar Neja a ranar 13 ga Oktoba 2023,” in ji shi.

Babban kwamandan runduna ta daya ta (GOC) kuma kwamandan rundunar ‘Operation WHIRL PUNCH’ Manjo Janar Valentine Okoro ya bayyana jin dadinsa da nasarorin da aka samu a hare-haren, ya kuma yabawa sojojin bisa wannan kwazon da suka nuna.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Fashin dajiJihar NejaKadunaRundunar sojin ruwan Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Next Post

Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

15 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

16 hours ago
Next Post
Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB

Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.