• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 151, Sun Kama 456, Sun Kubutar Da 67

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar Hukumar Tsaro ta kasa (DHQ) a ranar Alhamis ta ce, dakarun sojoji da aka tura aiki sassan kasar nan, sun samu nasarar hallaka ‘yan ta’adda 151 tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su 76, kuma sun cafko ‘yan ta’adda 456 a sameme daban-daban da suka aiwatar a cikin mako guda tak.

Daraktan sashin yada labarai na hukumar tsaron, Manjo Janar Edward Buba, shi ne ya sanar da hakan yayin da ya ke ganawa da manema labarai kan ayyukan da sojojin suka aiwatar, inda ya ce, wasu mutum 45 da ake zargin barayin Danyen Man fetur ne, su ma an kamasu yayin da kuma aka kwato mai da darajarsa ya kai Naira Biliyan N1,011,851,250 da suka sace.

  • Sojoji Sun Ceto Mutum 18 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Arewa Maso Yamma

Ya ce, sojojin sun kuma kwato makamai daban-daban har guda 216 da alburusai 443.

Da yake jero makamai da kayayyakin da sojojin suka kwato, Buba ya ce, an kwato bindiga kirar AK47 guda 62, bindiga mai amon harsasai guda 7, harbi ka noke guda 19, fistol guda 3, wasu bindiga kirar gida guda 10, fistol kirar gida 5, nakiya (IED) guda 399, harsasai masu rai samfurin 7.62mm special ammo guda 225, alburusai samfurin 7.62mm NATO guda 10, alburusai samfurin 9mm ammo guda 13, harsasai 7.62mm x 54mm guda 20, harsasai samfurin cartridges guda 57, 49 magazines, motoci 21, machine hudu, keke-napep daya, wayoyin salula ukulele, da kudi da yawansu ya kai N3,194,450.00.

Kazalika, sojojin da ke aiki a yankin Neja-Delta sun gano gami da tarwatsa gidajen karkashin kasa guda 21, jiragen ruwa 56, tukwanan adana abinci 138, nau’in abun dumama abinci (oven) guda 235, injunan ban ruwa 6, wasu jirgin ruwa guda 2 masu gudun tsiya, haramtatun wuraren tace mai 89 da kudi naira N13,950.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sannan kuma sojojin sun kamo litar danyen mai 1,205,950 da aka sace, litar gas 452,910, litar man fetur  guda 22,650 da kuma litar kananzir 3,000.

Ya ce, sojoji ba za su daina kokarin da su ke yi ba na dakile aniyar bata gari da ‘yan ta’adda ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lantarki Ya Ɗauke A Faɗin Nijeriya, Yayin Da Tashar Samar Da Wuta Ta Ƙasa Ta Lalace

Next Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

20 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.