Ƙoƙarin babbar jam’iyyar adawa ta PDP na sulhunta mambobinta gaban zaben 2027 ya fuskanci koma baya lokacin da Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya fice daga yarjejeniyar zaman lafiya ta jam’iyyar. Wike, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa ya janye daga dukkan yarjejeniyoyin sulhu da aka cimma a baya a cikin jam’iyyar PDP.
Matsalolin da ke addabar jam’iyyar PDP sun kara tsananta bayan da Wike ya janye daga duk wata yarjejeniya ta sulhu da aka taba cimmawa a cikin jam’iyyar adawar.
- Wike Ya Musanta Jita-jitar Faɗuwa Ta Rashin Lafiya
- Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Wike dai ya dora alhakin rikicin PDP a kan gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, yana mai gargadin cewa rashin bin yarjejeniyoyin da aka cimma ne ke haddasa rikicin jam’iyyar, kuma ya bayyana Makinde a matsayin wanda ya fi haddasa wannan matsala.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na D, Wike ya zargi manyan shugabannin jam’iyyar, ciki har da Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah, da cin amanar juna da rashin gaskiya da kuma karya yarjejeniyoyi da dama da aka cimma a baya.
Yayin da yake bayani kan asalin rikicin PDP tun bayan kammala zaben 2023, Wike ya zargi Makinde da gurbata dukkan kokarin sasanci da zaman lafiya a cikin jam’iyyar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp