• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tagomashi Da Alfanun Kiyaye Al’adar Ziyartar Afirka A Farkon Shekara Da Ministan Harkokin Wajen Sin Ke Yi

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

Kasar Sin na kiyaye wata al’ada ta tsawon shekaru 35 a fannin diflomasiyya, wato a farkon kowace shekara, ministan harkokin wajen kasar kan yi ziyararsa ta farko a nahiyar Afirka. A wannan shekara ma haka aka yi, inda daga ranar 5 zuwa 11 ga wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ziyarci kasashen Namibia da Congo Brazzaville da Chadi da ma Nijeriya, bisa goron gayyatar da aka yi masa. 

Wani abokina dan Nijeriya ya taba min tambaya, shin me ya sa ministocin harkokin wajen kasar Sin suka yi ta kiyaye wannan al’ada? Muna iya gano amsar tambayar daga zancen da Mr.Wang Yi ya yi lokacin da yake ziyara a kasar Namibia. A yayin zantawa da shugabar kasar Netumbo Nandi-Ndaitwah, Wang Yi ya ce, ”Ta hanyar kiyaye wannan al’ada ta kai ziyararmu ta farko a kasashen Afirka a farkon kowace shekara, muna son shaida wa duniya cewa, a duk irin sauye-sauye ko yanayin da ake ciki a duniya, kullum kasar Sin za ta kasance aminiyar da kasashen Afirka suka yi amanna da kuma dogaro da ita a kokarinsu na tabbatar da ci gabansu, haka kuma kasa ce da ke mara musu baya a dandalin kasa da kasa. ”

  • Zargin Safarar Kananan Yara: Gwamnatin Kano Ta Karbi Yara 59 Da Aka Kama A Hanyar Zuwa Nasarawa
  • An Nemi Sojoji Su Kara Jajircewa Wajen Gudanar Da Ayukansu

Yadda kasar Sin ta furta ke nan, kuma hakan take aikatawa. Idan ba mu manta ba, a zamanin da kasashen Afirka ke gwagwarmayar neman ‘yancin kansu, kasar Sin ta nuna tsayayyen goyon bayanta tare da samar da gudummawarta gare su. Bayan da suka samu ‘yancin kansu kuma, kasar Sin ta ci gaba da tallafa musu a kokarinsu na kiyaye ikon mulkin kansu da kuma raya tattalin arzikinsu. Ya zuwa karshen shekarar 2023, yawan kudaden jarin da kasar Sin ta zuba wa kasashen Afirka ya zarce dala biliyan 40, ta kuma taimaka wajen gina hanyoyin mota na tsawon kilomita dubu 100 da layukan dogo na sama da tsawon kilomita dubu 10 da gadoji kusan dubu da ma tashoshin jiragen kasa kusan dari a Afirka. Haka nan, ko a cikin shekaru 3 kadai da suka wuce, ta samar da guraben aikin yi fiye da miliyan daya a Afirka. Kasar Sin ita ce ta farko da ta bayyana goyon bayanta ga shigar da kungiyar tarayyar Afirka a matsayin mamban kungiyar G20. Lallai jerin nasarorin da aka cimma sun shaida huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka, kuma yadda kasar Sin take cika alkawuranta a kullum ya kasance sanadin dimbin nasarorin da aka cimma.

A gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka(FOCAC) da ya gudana a watan Satumban bara a birnin Beijing, kasar Sin da dukkanin kasashen Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da ita sun sanar da daukaka huldarsu. To, wannan sabon mafarin huldarsu ya sa ziyarar ministan wajen kasar Sin kasashen Afirka a wannan karo ya sha bamban da na baya, wato ziyarar na da nufin tabbatar da sakamakon da aka cimma a gun taron kolin dandalin FOCAC, da kuma kara inganta hadin gwiwarsu a fannoni daban daban.

Don haka, bayan da ya gana da shugaban kasar Congo Brazzaville Denis Sassou-Nguesso, Wang Yi ya ce, ”Dalilin wannan ziyara shi ne don mu tattauna tare da Congo Brazzaville, domin mu cimma daidaito a kan yadda za a kara inganta hadin gwiwarmu karkashin tsarin dandalin FOCAC. ” An ce, bayan tattaunawa tare da Congo Brazzaville, wadda ta kasance kasar da ke shugabantar dandalin FOCAC tare da kasar Sin a wannan karo, sassan biyu sun tsara jadawali da ma taswira game da tabbatar da sakamakon da aka cimma a taron dandalin FOCAC nan da shekaru uku masu zuwa. Misali, a bana, sassan biyu za su kira taron ministoci na tabbatar da sakamakon taron dandalin, don sa kaimin cimma nasarorin hadin gwiwarsu da wuri. Sa’an nan a shekarar 2026, sassan biyu za su gudanar da bukukuwa na murnar cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Afirka da musayar al’adu a tsakaninsu, haka kuma za a kira taron manyan jami’ai karo na 18 na dandalin FOCAC, don gaggauta tabbatar da sakamakon da aka cimma.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Har wa yau, a lokacin ziyararsa, Wang Yi ya ce, kasar Sin na son sa kaimin aiwatar da shawarar kiyaye tsaron duniya ta yadda za ta haifar wa Afirka da mai ido. ”Za mu kulla kawance da kasashen Afirka wajen tabbatar da shawarar kiyaye tsaron duniya, tare da sa kaimin aiwatar da shirin hadin gwiwar kiyaye tsaro. Za mu samar da gudummawar soja na yuan biliyan ga kasashen Afirka, tare da taimaka wa kasashen Afirka horar da kwararrun soja 6,000 da ‘yan sanda 1,000…”, in ji shi. Ban da haka, ya ce, kasar Sin tana so hada kai da kasashen Afirka wajen tabbatar da shirin samar da makamashi mai tsabta da aka gabatar a gun taron kolin dandalin FOCAC, da raya ayyukan samar da wutar lantarki ta makamashin hasken rana, don taimaka wa kasashen Afirka tabbatar da bunkasar tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba.

Kyan alkawari cikawa, kullum kasar Sin na cika alkawuranta na tallafa wa kasashen Afirka wajen tabbatar da ci gabansu. Bisa wannan ziyarar ta ministan harkokin wajen kasar Sin a kasashen Afirka, an tsara jadawali da taswira game da hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka nan da shekaru uku masu zuwa, kuma tabbas hadin gwiwarsu zai kara haifar da da mai ido a yayin da suke kokarin zamanantar da kansu. (Lubabatu Lei)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Next Post
Masana Kimiyyar Sin Sun Samu Ci Gaba A Binciken Sarrafa Batirin Lithium

Masana Kimiyyar Sin Sun Samu Ci Gaba A Binciken Sarrafa Batirin Lithium

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.