• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gidajen Sarautar Da Suka Mulki Katsina

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
Tarihin Gidajen Sarautar Da Suka Mulki Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Katsina tana da tarihi mai yawa musamman na masarautun da suka yi mulkin Katsina tun farko ya zuwa yanzu, ga dai yadda Masarautun su ke.

Gidan Sarauta na Durbawa
Gidan Sarautar Durbawa shi ne asalin wadanda suka fara Sarautar Katsina. Ance an samu sunan Katsina ne bayan da wata ‘yar Sarki daga Daura wadda ta auri Janzama wanda shine Sarkin Durbawa,da ya yi mulki daga Durbi-Takusheyi wanda kuma har yanzu sunan shi an aje shi kamar dutse kusa da Mani.Babu dai wani bayanin da aka rubuta dangane da wadanda suka yi Sarauta a karkashn Masarautar.Amma Janzama shi ne wanda ya yi mulki na karshe a karkashin daular Durbawa. Kumayau ne wanda ya raba shi da mulki shi ne Sarki na farko a daular Kumayau.

Gidan Daular Kumayau
Wannan ita ce daula ta biyu bayan daular Durbawa,ta samar da Sarakunan bakwai daga Kumayau zuwa Sanau.Ita wannan daular ana nada Sarki ne ta hanyar yin kokawa inda wand ya yi nasara shi ne ake zaba sabon Sarki.

Gidan Daular Korau
Daular Korau ta samar da Srakunan Katsina 31 wanda aka fara daga Muhammadu Korau wanda shi ne Sarki na farko da yake musulmi a karkashin daula ta uku bayan ya samu nasara akan Sanau,tun daga wancan lokacin sai maganar Sarauta kuma ta koma ta gado aka barta ga sai wadanda suka gaji Sarauta.

Gidan Daular Dallazawa
An samu wannan daular ne a sanadiyar Jihadin Shehu Usman Danfodio a shekarar 1804.Jihadin ne a karkashin Malam Ummarun Dallaje,Malam Mammam Na Alhaji Malam Ummarun Dunyawa wadanda suka amshi tuta daga Malam Muhammadu Bello dan Shehu Usman Danfodiyo a madadin shi.Daular ta samar da Srakunan Katsina takwas daga Malam Ummarun Dallaje (1807)zuwa Malam Yaro a shekarar 1906.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

Gidan Daular Sullubawa
Ita ce daula ta hudu bayan daular Durbawa,bayan da aka tunbuke Sarki Abubakar da Malam Yero wanda Turawan mulkin mallaka suka yi wannan shi ya bada dama ta mulkin Sullubawa ko kuma ace daular Dikko.Wannan daula ta samar da Sarakuna hudu daga Sarkin Katsina Muhammadu Dikko a shekarar 1906 zuwa Sarkin Katsina Abdulmuminu Kabir Usman Sarki na yanzu.

Sarakunan Habe
Gidan Durdawa
1.Sarkin Katsina Kumayau 2.Sarkin Katsina Rumba Rumba 3.Sarkin Katsina Bataretare 4.Sarkin Katsina Jin Marata
5.Sarkin Katsina Yankatsari 6. Sarkin Katsina Jibda Yaki (Sanau)

Gidan Korau
7.Muhammadu Korau 1348 – 1398
8.Usman Maje 1398 – 1405 (9). Ibrahim Soro 1405 – 1408(10) Marubuci 1408 – 1426
11.Muhammadu Turare 1426 – 1436
12.Ali Murabus 1436 – 1462(13) Ali Karya 1462 – 1475(14) Usman Tsaga Rana 1475 – 1525
15.Usman Damisa Gudu 1525 – 1531
16. Ibrahim Maje 1531 – 1599
17. Malam
18. Yusufu 1599 – 1613
19. Abdulkadir 1613 – 1615

20.Ashafa 1615 – 1615(21) Gabdo 1615 – 1625

22.Muhammadu Wari 1625 – 1637.

23.Muhammadu Tsaga Rana 1637 – 1649

24.Mai Daraye 1649 – 1660

25. Sulaiman 1660 – 1673

26. Usman Tsaga Rana 1673 – 1692

27.Toyariru 1692 – 1705

28. Yanka Tsari

29. Uban Yara I 1705 – 1708

30. Uban Yara II 1708 – 1740

31. Jan Hazo (Dan Uban Yara) 1740 – 1751

32. Tsaga Rana 1751 – 1764

33.Muhammadu Kayiba 1764 – 1771

34. Karya Giwa 1771 – 1788

35. Giwa Agwaragi 1788 – 1802

36. Gozo 1802 – 1804

37.Bawa Dan Giwa 1804 – 1805

38. Muhammadu Maremawa 1805 – 1806

39.Magajin Haladu 1806 – 1807

Sarakunan Fulani

Dallazawa:

40.Umarun Dallaje 1807 – 1835

41. Muhammadu Bello 1835 – 1844

42.Saddiƙu 1344 – 1869 Ahmadu Rufa’i

43. 1869 – 1869

44). Ibrahim 1869 – 1882

45.Musa 1882 – 1887

46. Abubakar 1887 – 1905

47. Yero 1905 – 1906

Sullubawa

48.Muhammadu Dikko 1906 – 1944

49.Usman Nagogo 1944 – 1981

50.Muhammad Kabir Usman 1981-2008

51.Abdulmumini Kabir Usman 2008 zuwa yanzu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'ajabiMasarautar HadejiaSarauta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Liu Jianchao Ya Ziyarci Kasar Amurka

Next Post

Xi Jinping Ya Bukaci Hukumomin Shari’a A Kasar Su Karfafa Farfadowar Kasar Sin

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

40 minutes ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

57 minutes ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

5 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

13 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Bukaci Hukumomin Shari’a A Kasar Su Karfafa Farfadowar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Bukaci Hukumomin Shari’a A Kasar Su Karfafa Farfadowar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.