• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Kasar Sin: Yabon Gwani Ya Zama Dole

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Shugaban yankin Zanzibar na kasar Tanzaniya, Hussein Ali Mwinyi ya ba da lambobin yabo da takardun shaidar karramawa ga daukacin mambobin tawaga ta 33 ta jami’an lafiya na Sin, da suka bayar da gudunmawar jinya da kiwon lafiya a Zanzibar.

 

Kiwon lafiya daya ne daga cikin bangarorin da Sin take hadin gwiwa da kasashen Afrika, inda ta kan tura jami’ai akai-akai domin bada tallafin jinya da horo kyauta. Hadin gwiwar kasar Sin ba abu ne dake mayar da hankali kan moriyarta kadai ba, sabanin yadda wasu suke yada jita jita ko ma suke yi, kasar Sin ta kan taimaka ta kowane bangare da take ganin kasashe masu tasowa, musamman na Afrika na da bukata domin ganin sun samu ci gaba.

  • Wang Yi Da Jake Sullivan Sun Gudanar Da Sabon Zagaye Na Muhimmin Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Tun daga shekarar 1963, kasar Sin ta fara tura jami’an kiwon lafiya kasashen duniya. Cikin shekaru 60 da suka gabata, ta tura jami’an da yawansu ya kai 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, tare da jinyar mutane miliyan 290. Kuma yayin da wadannan jami’an lafiya ke zuwa kasashen, su kan tafi da magunguna da kayayyakin jinya da gwaje-gwaje da sauransu, domin tabbatar sun bada ingantaccen kiwon lafiya.

 

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

A kwanakin baya, na hadu da wata kwararriyar likitar ido ta kasar Sin mai suna Dr. Li Yun. Tun daga shekarar 2016, Li Yun ta je nahiyar Afrika sau 4, inda ta gudanar da tiyatar ido fiye da 500. Kuma duk da cewa ta dawo kasar Sin, har yanzu ba ta yanke hulda da kasashen da ta je, har yanzu ta kan tattauna da su ko gudanar da taron karawa juna sani kan abubuwan da suka shige musu duhu.

 

Yanzu haka akwai tawagogin lafiya na Sin dake aiki a wurare 115 dake kasashe 56 na fadin duniya, kuma galinbinsu wurare ne masu nisa da koma baya. Duba da irin ci gaban kasar Sin da kyautatuwar yanayin rayuwa, wadannan jami’ai sun cancanci yabo matuka, domin sun sadaukar da kansu da jin dadinsu wajen ganin sun taimakawa burin kasarsu na ganin ta taimakawa masu bukata. A kullum na kan ce, daya daga cikin tubalin ci gaban kasar Sin shi ne, yadda al’ummarta ke da kishi da kaunar kasarsu da kuma kyakkyawar fahimta da hadin gwiwa dake akwai tsakanin gwamnati da al’umma. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

LABARAI MASU NASABA

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.