• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Amince Da Biyan Kuɗin Kafa Cibiyar Yaɗa Labarai Ta UNESCO

by Sulaiman
11 months ago
Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da fitar da kuɗaɗe domin kafa Cibiyar Yaɗa Labarai ta UNESCO (Media and Information Literacy Institute, MIL) a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a lokacin wani taro da suka yi da Mataimakin Darakta-Janar na UNESCO, Dakta Tawfik Jelassi, a birnin Paris na ƙasar Faransa.

  • Google, Microsoft, TikTok Sun Biya Gwamnatin Nijeriya Harajin N2.55trn A 2024 – NITDA
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Fahimtar Kasar Sin 

Idris, wanda ya bayyana hakan a gefen ziyarar da Shugaba Tinubu ya kai ƙasar Faransa, ya bayyana irin goyon bayan da Shugaban Ƙasar ke bai wa aikin.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Ya ce:“Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba da goyon baya sosai ga aikin, kuma ya amince da fitar da duk wasu kuɗaɗen da ake buƙata domin cibiyar ta fara aiki nan take, wadda za ta kasance a Babban Birnin Tarayya.”

 

Ministan ya nuna jin daɗin sa ga UNESCO da ta bai wa Nijeriya haƙƙin kafa Cibiyar ta MIL, wadda ita ce kaɗai irin ta a duniya.

 

Ya tuna ganawar da ya yi da Dakta Jelassi a shekarar 2023, tare da jaddada aniyar Nijeriya na ganin cibiyar ta samu nasara.

 

Jelassi ya bayyana jin daɗin sa game da kafa cibiyar a Nijeriya tare da nanata muhimmancin sa wajen magance matsalolin da suka haɗa da yaɗa labaran ƙarya, da kalaman ƙiyayya. Ya kuma bayyana ƙoƙarin UNESCO na samar gidan yana mai aminci.

 

Har ila yau, ya gabatar da shirin UNESCO MIL Cities, wanda ke haɗa ilimin yaɗa labarai a cikin ayyukan birane, waɗanda suka haɗa da harkokin sufuri da al’adu.

 

Idris ya yi maraba da manufar MIL Cities kuma ya yi alƙawarin cewa Nijeriya za ta taka rawar gani ta hanyar zaɓar wani birni don aiwatar da matakin farko na shirin.

 

Ministan ya kuma ba da tabbacin cewa Nijeriya za ta yi amfani da ƙa’idojin UNESCO don Gudanar da Kafafen Gidan Yana, wanda ke da nufin inganta tunani da gaskiya tare da kare ‘yancin faɗin albarkacin baki.

 

Idris ya samu rakiyar Jakadiyar Nijeriya kuma Babbar Wakiliya ga UNESCO, Dr. Hajo Sani, zuwa taron da aka gudanar a hedikwatar UNESCO.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Yadda Za A Samu Sabuwar Damar Neman Ci Gaba Tare Bisa Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Yadda Za A Samu Sabuwar Damar Neman Ci Gaba Tare Bisa Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.