• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa

by El-Zaharadeen Umar
12 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Izala na Jihar Katsina, Sheikh Yakubu Musa Hassan, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, da ya binciki kuɗaɗen da abinci da ake bai wa gwamnonin jihohi domin raba wa talakawa.

Malamin ya bayyana haka ne, a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a gidansa da ke Katsina, dangane da zanga-zangar yunwa da matsin rayuwa da matasa ke yi a Nijeriya.

  • Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
  • Ndume Ya Ba Ganduje Haƙuri Kan Kalaman Da Ya Yi Kan Tinubu Da Suka Yi Sanadin Sauke Shi

Malamin ya ƙara da cewa gaskiyar magana ita ce wannan taimako shugaba Tinubu yake bayarwa baya kai wa da talakawa.

Haka kuma ya yi kira ga waɗanda aka ɗora wa amanar al’umma musamman gwamnoni da su ji tsoron Allah wajen rabon tallafin da Gwamnatin Tarayya ke bayarwa.

“Ina kira ga ‘yan siyasa da kada su riƙa boye abincin da ake ba su, suna siyasa da shi, ina so ku sani, hatta ayyukan tituna da kuke yi idan yunwa ta kashe mutane wa za ku yi wa aikin?” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

A cewarsa, a irin wannan yanayi da ƙasa da al’umma suka tsinci kansu, ya kamata a ɗebo kuɗi daga ko ina domin magance wannan matsala ta yunwa da matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita.

Kazalika, ya ce duk gwamnan da aka bai wa irin wannan kuɗaɗen da kayan abinci domin a fitar da al’umma daga cikin wannan yanayi, ya ce su ji tsoron Allah su isar da wannan sako ga waɗanda abin shafa.

Da juya kan batun zanga-zanga, malamin ya ce akwai takaici irin yadda matasa suka koma barayi suna kwashe duniyoyin al’umma da sunan zanga-zanga.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar sun kama duk wanda ya taɓa kayan jama’a domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

“Irin wannan abubuwan ne muka hango tun kafin a fara wannan zanga-zanga amma wasu suka riƙa zagin Malamai cewa an ba su kuɗi ne su hana matasa yin zanga-zanga, a zahirin gaskiya maganar ba haka ta ke ba,” a cewarsa.

Ya ƙara jaddada cewa lallai ya kamata Gwamnatin Tarayya da kuma na jihohi da sake karatun ta nutsu kan batun matas, a yi sabon tunani game da makomarsu ta hanyar fitowa da sabbin tsare-tsare na gwamnatin domin koya masu sana’a da ba su jari.

Ya ce a matsayinsu na malamai duk abin da ya taso suna iya baƙin ƙoƙarinsu domin ganin an warware komai cikin maslaha.

Malamin ya ce ‘yan jaridu suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ganin an kawo karshen wannan zanga-zanga fiye da gwamnati da kuma jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa idan ‘yan jaridu suka yi amfani da alƙalumansu da hikimar da Allah Ya ba su, lallai za su iya kashe wutar zanga-zangar ake yi a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeGwamnoniIzalaKatsinaMalamiMatasaTallafiTinubuZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamala Harris Ta Zabi Tim Walz A Matsayin Mataimaki Kafin Shiga Zaben Amurka 

Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

1 hour ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

18 hours ago
Next Post
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.