• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Izala na Jihar Katsina, Sheikh Yakubu Musa Hassan, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, da ya binciki kuɗaɗen da abinci da ake bai wa gwamnonin jihohi domin raba wa talakawa.

Malamin ya bayyana haka ne, a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a gidansa da ke Katsina, dangane da zanga-zangar yunwa da matsin rayuwa da matasa ke yi a Nijeriya.

  • Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
  • Ndume Ya Ba Ganduje Haƙuri Kan Kalaman Da Ya Yi Kan Tinubu Da Suka Yi Sanadin Sauke Shi

Malamin ya ƙara da cewa gaskiyar magana ita ce wannan taimako shugaba Tinubu yake bayarwa baya kai wa da talakawa.

Haka kuma ya yi kira ga waɗanda aka ɗora wa amanar al’umma musamman gwamnoni da su ji tsoron Allah wajen rabon tallafin da Gwamnatin Tarayya ke bayarwa.

“Ina kira ga ‘yan siyasa da kada su riƙa boye abincin da ake ba su, suna siyasa da shi, ina so ku sani, hatta ayyukan tituna da kuke yi idan yunwa ta kashe mutane wa za ku yi wa aikin?” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A cewarsa, a irin wannan yanayi da ƙasa da al’umma suka tsinci kansu, ya kamata a ɗebo kuɗi daga ko ina domin magance wannan matsala ta yunwa da matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita.

Kazalika, ya ce duk gwamnan da aka bai wa irin wannan kuɗaɗen da kayan abinci domin a fitar da al’umma daga cikin wannan yanayi, ya ce su ji tsoron Allah su isar da wannan sako ga waɗanda abin shafa.

Da juya kan batun zanga-zanga, malamin ya ce akwai takaici irin yadda matasa suka koma barayi suna kwashe duniyoyin al’umma da sunan zanga-zanga.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar sun kama duk wanda ya taɓa kayan jama’a domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

“Irin wannan abubuwan ne muka hango tun kafin a fara wannan zanga-zanga amma wasu suka riƙa zagin Malamai cewa an ba su kuɗi ne su hana matasa yin zanga-zanga, a zahirin gaskiya maganar ba haka ta ke ba,” a cewarsa.

Ya ƙara jaddada cewa lallai ya kamata Gwamnatin Tarayya da kuma na jihohi da sake karatun ta nutsu kan batun matas, a yi sabon tunani game da makomarsu ta hanyar fitowa da sabbin tsare-tsare na gwamnatin domin koya masu sana’a da ba su jari.

Ya ce a matsayinsu na malamai duk abin da ya taso suna iya baƙin ƙoƙarinsu domin ganin an warware komai cikin maslaha.

Malamin ya ce ‘yan jaridu suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ganin an kawo karshen wannan zanga-zanga fiye da gwamnati da kuma jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa idan ‘yan jaridu suka yi amfani da alƙalumansu da hikimar da Allah Ya ba su, lallai za su iya kashe wutar zanga-zangar ake yi a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeGwamnoniIzalaKatsinaMalamiMatasaTallafiTinubuZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamala Harris Ta Zabi Tim Walz A Matsayin Mataimaki Kafin Shiga Zaben Amurka 

Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

8 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

9 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

14 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

16 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.