• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Gangami Yakin Neman Ilimi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Ilimi

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kaddamar da gangamin yakin neman bunkasa ilimi da koyon aikin hannu da kuma na daidaiton jinsi.

Gangamin mai taken “Dukkaninmu Daya Muke” kungiyar matan shugabannin kasashen Afrika (OAFLAD) ce ta gabatar da tsarawa.

  • Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi
  • Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano

 An kaddamar da gangamin a kasashe 15 da ke da manufar bunkasa harkokin kiwon lafiya, ilimi, samar wa mutane ababen dogaro da kai na sana’o’i, da kuma yaki da cin zarafin jinsi.

Nijeriya wacce ta dauki shirin wajen maida hankali kan taken cewa ilimi shi ne babban hanya na kawo canji, wanda matar shugaban kasa Sanata Senator Oluremi Tinubu ta gabatar.

Da yake kaddamar da gangamin a fadar shugaban kasa, Tinubu ya jinjina wa kokarin matan shugabannin kasashen Afrika, da suka kasance masu maida hankali wajen ganin an samu daidaiton jinsi da ke cikin matsalolin da yankin ke fama da shi.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

“Wannan gangamin na da matukar muhimmanci a garemu a nan Afrika, don haka, ina tayaku murna, musamman matata Senator Oluremi Tinubu, wacce ta kasance ta zabi bangaren ilimi a matsayin abu na farko da ganganmin zai maida hankali a kansa a fadin kasar nan.

“Manufar kaddamar da wannan gangamin a Nijeriya shi ne, babban hanya na kawo sauyi, muhimmin lamari ne wajen ci gaban Afrika, idan muka samu nasarar wajen daidaiton jinsi da tabbatar da damarmaki ga kowa.

“Dole mu ci gaba da samar da hanyoyi na damarmaki ga dukkanin yaranmu wajen ganin sun samu damar samun ilimi ba tare da barin kowa a baya ba, musamman yara mata.

“Dole ne mu samar da al’umma da babu bambancin jinsi da kowa zai kasance na samun dama kamar kowa, ba tare da la’akari da waye ba, saboda ta hakan za mu iya gina al’umma mai cike da kwanciyar hankali ga kowa,” ya shaida.

 A cewarsa, shirin wani dama ne karo na biyu wajen ganin an rage kaifin matsalar yaran da ba su zuwa makaranta domin ganin sun koma zuwa makaranta wajen tunkarar yadda za su kyautata rayuwarsu na gaba.

Tinubu ya yi alkarin cewa nan ba da jimawa ba ta karkashin hukumar kula da ilimi a matakin farko za a samu nasarar gina wasu makarantu ta yadda za a ci gaba da dakile matsalolin da suke akwai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
Labarai

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Dan Majalisar Wakilai, Aminu Sani Jaji A Zamfara

Da Dumi-Dumi: APC Ta Kori Dan Majalisar Wakilai, Aminu Sani Jaji A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

Iwobi Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Firimiya

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.