• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

by Muhammad and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Farfesa Yahaya Isa Bunkure a matsayin sabon Shugaban Jami’ar Ilimi Ta Tarayya da ke Zariya (FUEZ), Jihar Kaduna.

 

Farfesa Bunkure, fitaccen masani ne a fannin koyar da kimiyya, kuma shi ne yake rike da muƙamin Shugaban Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano a halin yanzu. Sanarwar naɗinsa ta fito ne a ranar Laraba daga mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga.

Jami’ar Tarayya ta Ilimi, Zariya, na daya daga cikin tsofaffin Kwalejojin Ilimi na Tarayya guda huɗu da aka ɗaukaka zuwa matsayin cikakkun jami’o’i a tsakanin shekarar 2022 zuwa 2023. A bisa ga dokokin da suka shafi jagorancin jami’o’i, shugaban jami’a zai yi wa’adin shekaru biyar.

A wani labarin kuma, Shugaba Tinubu ya amince da naɗin wasu muƙamai a fannin ilimi, inda ya naɗa Injiniya Abdurrazaq Abubakar Nakore a matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ilimi ta Tarayya Yusuf Maitama Sule da ke Kano. Har ila yau, ya naɗa Farfesa Abdullahi Tukur Kodage a matsayin sabon shugaban jami’ar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

Nakore, memba ne na ƙungiyar Injiniyoyin Nijeriya (NSE), kuma ya taɓa rike muƙamin Sakataren Zartarwa na Hukumar Wutar Lantarki a karkara a Jihar Jigawa. Farfesa Kodage kuwa, kwararre ne a fannin ilimi da yake da gogewa a harkar koyarwa da al’amuran gudanarwa.

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa waɗannan naɗe-naɗen na daga cikin ƙoƙarin da gwamnati take yi domin ƙarfafa shugabanci a tsarin ilimi da kuma tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da sababbin jami’o’in da aka ɗaukaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Next Post

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Related

Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

21 minutes ago
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa
Manyan Labarai

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

51 minutes ago
Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

1 hour ago
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

2 hours ago
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

11 hours ago
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

14 hours ago
Next Post
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

LABARAI MASU NASABA

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

September 26, 2025
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

September 26, 2025
Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

September 26, 2025
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

September 25, 2025
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

September 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

September 25, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

September 25, 2025
Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.