Shugaban kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan dokar karin albashi da alawus ga ma’aikatan shari’a ta 2024.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, sabuwar dokar ta tanadi karin albashi da alawus-alawus ga ma’aikatan shari’a na kasa.
Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin majalisar dattawa, Sanata Basheer Lado, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Talata da yamma, ya bayyana cewa, rattaba hannun wani yunkuri na musamman wanda ya nuna jajircewar Tinubu tare da fifita jin dadin ma’aikatan Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp