Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya taya shugaban kasa Bola Tinubu murnar cika shekaru biyu akan karagar mulki, yana mai cewa yayin da jam’iyya da gwamnati ke murna amma ya kamata a tunatar da ‘yan kasa cewa, shugabanci abu ne mai gudana.
Buhari, a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya fitar, ya bukaci da a bai wa gwamnatin APC hadin gwiwa a daidai lokacin da Tinubu ke cika shekara biyu a kan karagar mulki, inda ya bayyana cewa, ana samun nasara a hankali ne bayan gyara amma ba a dare daya ba.
- Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
- Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Hukunta Matasa Masu Janyo Rikice-Rikice
Buhari ya bayyana goyon bayansa ga kokarin da gwamnatin ke yi na dakile talauci da hauhawar farashin kayayyaki, wanda a cewarsa ya fi shafar iyalai masu karamin karfi, amma duk da haka, bai kamata a bar aikin rage radadin talauci da hauhawar farashin kayayyaki ga gwamnati kadai ba.
“Kamfanoni masu zaman kansu da kuma dukkanmu a matsayinmu na ‘yan kasa dole ne mu hada hannu wajen taimakawa gwamnati,” in ji tsohon shugaban.
Ya bukaci ‘yan Nijeriya da su kasance masu kyakkyawan fata kuma su kasance da kwarin gwiwa game da makomar kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp