• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A siyasance, kowa yana so a ce shi ne babba, inda jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya fito fili ya nuna cewa shi ne babba a tsakaninsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Mista Peter Obi.

Wannan takaddama ta kunno kai ne tun lokacin da wasu masu ruwa da tsaki suka bukaci Kwankwaso ya amince da shirinsu na zama a abokin takarar Obi a zaben shugaban kasa a 2027.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Matasa 3 Sun Shiga Hannu Kan Kashe Wani Mutum Don Mallakar Filinsa A Kano

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda kuma shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya ce yana jira ya ga ka’idojin da za a yi amfani da su wajen gudanar da irin wannan tsarin, duba da irin iliminsa da siyasa a kan Obi.

A wani faifan bidiyo da ya yi ta yawo a kafafen sada zumunta a ranar Asabar, an ga Kwankwaso na bayyana cewa, “Na fi Peter Obi girma a siyasance. Ni babban yayansa ne. Ina da kwarewa fiye da shi. Na yi kokari fiye da shi lokacin da nake gwamnan jihata.

“Ba ni da matsala wajen zama mataimakin takarar Peter Obi, amma sai dai idan an cika wasu sharudda,” in ji shi, yana mai jaddada cewa duk wani kawancen da za a iya kullawa dole ne a gina shi bisa amana.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ya kara da cewa, “A shirye muke mu tattaunawa, muddin aka amince da sharuddanmu,” in ji shi, wanda ke nuna cewa shi da Obi a shirye suke su kulla kawancen siyasa da shugabancin jam’iyyar LP a gabanin zaben 2027.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi ne ya zo na uku a zaben da ya gabata da kuri’u 6,101,533, yayin da Kwankwaso ya taka rawar gani a jiharsa ta Kano, ya samu kuri’u 1,496,687 a kananan hukumomi 38 daga cikin 44 na jihar.

Kwankwaso ya kuma kasance mai sukar gwamnatin Shugaban kasa Bola Tinubu, musamman game da rabon kayan tallafin shinkafa a Jihar Kano. Ya zargi gwamnatin tarayya da kin bai wa gwamnatin jihar tallafin tare da mika wa ga ‘yan jam’iyyar adawa ta APC a jihar.

“Abun takaicin ne yadda gwamnatin tarayya ta raba tallafin shinkafa ga jihohi 35 a hannun gwamnoninsu, in ban da Jihar Kano wanda ak mika kason ga jiga-jigan APC. Wannan babban cin fuska ne ga dimokuradiyyar da kuma tsarin mulkinmu,” in ji Kwankwaso a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Tuwita.

Sai dai kuma, tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ya mayar wa da Kwankwaso martini, inda ya bayyana cewa Obi ne babba a siyasance fiye da Kwankwaso.

Ahmad, a cikin wani rubutu a shafinsa na Tuwita, ya ce duk da cewa ya kasance yana girmama Kwankwaso a matsayinsa na dan siyasa mai ci gaba, ba zai iya yin bara’a da furucin nasa ba.

Ya rubuta cewa, “Duk da cewa ban taba zama mai biyayya ga Kwankwasiyya ba, amma a ko da yaushe ina girmama Sanata Rabiu Kwankwaso kuma ina ganinsa a matsayin jiga-jigan dan siyasar da muke da su a kasar nan da ke samun ci gaba.

“Duk da haka, ban yarda da furucin da ya yi kwanan nan ba a lokacin da yake tattaunawa da shi a Kano, inda ya ce ya fi Peter Obi girma a siyasance. Idan aka dubi sakamakon zaben shugaban kasa na 2023, Peter Obi ya samu kuri’u 6,101,533 kuma ya yi nasara a jahohi 11, wanda ke nuna cewa ya samu goyon baya a kasatr nan. Sabanin yadda Sanata Kwankwaso ya samu kuri’u 1,496,687, wanda ya yi nasara a jiha daya kacal, Kano.

“Wadannan alkaluma sun nuna karara cewa, a kalla a yanayin zaben 2023, Peter Obi yana da matukar tasiri a siyasance a fadin kasar nan.

“Don haka Peter Obi ya fi Rabiu Kwankwaso girma a siyasance.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwankwasoObiSiyasatakara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.