• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A siyasance, kowa yana so a ce shi ne babba, inda jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya fito fili ya nuna cewa shi ne babba a tsakaninsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Mista Peter Obi.

Wannan takaddama ta kunno kai ne tun lokacin da wasu masu ruwa da tsaki suka bukaci Kwankwaso ya amince da shirinsu na zama a abokin takarar Obi a zaben shugaban kasa a 2027.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Matasa 3 Sun Shiga Hannu Kan Kashe Wani Mutum Don Mallakar Filinsa A Kano

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda kuma shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya ce yana jira ya ga ka’idojin da za a yi amfani da su wajen gudanar da irin wannan tsarin, duba da irin iliminsa da siyasa a kan Obi.

A wani faifan bidiyo da ya yi ta yawo a kafafen sada zumunta a ranar Asabar, an ga Kwankwaso na bayyana cewa, “Na fi Peter Obi girma a siyasance. Ni babban yayansa ne. Ina da kwarewa fiye da shi. Na yi kokari fiye da shi lokacin da nake gwamnan jihata.

“Ba ni da matsala wajen zama mataimakin takarar Peter Obi, amma sai dai idan an cika wasu sharudda,” in ji shi, yana mai jaddada cewa duk wani kawancen da za a iya kullawa dole ne a gina shi bisa amana.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya kara da cewa, “A shirye muke mu tattaunawa, muddin aka amince da sharuddanmu,” in ji shi, wanda ke nuna cewa shi da Obi a shirye suke su kulla kawancen siyasa da shugabancin jam’iyyar LP a gabanin zaben 2027.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi ne ya zo na uku a zaben da ya gabata da kuri’u 6,101,533, yayin da Kwankwaso ya taka rawar gani a jiharsa ta Kano, ya samu kuri’u 1,496,687 a kananan hukumomi 38 daga cikin 44 na jihar.

Kwankwaso ya kuma kasance mai sukar gwamnatin Shugaban kasa Bola Tinubu, musamman game da rabon kayan tallafin shinkafa a Jihar Kano. Ya zargi gwamnatin tarayya da kin bai wa gwamnatin jihar tallafin tare da mika wa ga ‘yan jam’iyyar adawa ta APC a jihar.

“Abun takaicin ne yadda gwamnatin tarayya ta raba tallafin shinkafa ga jihohi 35 a hannun gwamnoninsu, in ban da Jihar Kano wanda ak mika kason ga jiga-jigan APC. Wannan babban cin fuska ne ga dimokuradiyyar da kuma tsarin mulkinmu,” in ji Kwankwaso a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Tuwita.

Sai dai kuma, tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ya mayar wa da Kwankwaso martini, inda ya bayyana cewa Obi ne babba a siyasance fiye da Kwankwaso.

Ahmad, a cikin wani rubutu a shafinsa na Tuwita, ya ce duk da cewa ya kasance yana girmama Kwankwaso a matsayinsa na dan siyasa mai ci gaba, ba zai iya yin bara’a da furucin nasa ba.

Ya rubuta cewa, “Duk da cewa ban taba zama mai biyayya ga Kwankwasiyya ba, amma a ko da yaushe ina girmama Sanata Rabiu Kwankwaso kuma ina ganinsa a matsayin jiga-jigan dan siyasar da muke da su a kasar nan da ke samun ci gaba.

“Duk da haka, ban yarda da furucin da ya yi kwanan nan ba a lokacin da yake tattaunawa da shi a Kano, inda ya ce ya fi Peter Obi girma a siyasance. Idan aka dubi sakamakon zaben shugaban kasa na 2023, Peter Obi ya samu kuri’u 6,101,533 kuma ya yi nasara a jahohi 11, wanda ke nuna cewa ya samu goyon baya a kasatr nan. Sabanin yadda Sanata Kwankwaso ya samu kuri’u 1,496,687, wanda ya yi nasara a jiha daya kacal, Kano.

“Wadannan alkaluma sun nuna karara cewa, a kalla a yanayin zaben 2023, Peter Obi yana da matukar tasiri a siyasance a fadin kasar nan.

“Don haka Peter Obi ya fi Rabiu Kwankwaso girma a siyasance.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwankwasoObiSiyasatakara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.