• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A siyasance, kowa yana so a ce shi ne babba, inda jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya fito fili ya nuna cewa shi ne babba a tsakaninsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Mista Peter Obi.

Wannan takaddama ta kunno kai ne tun lokacin da wasu masu ruwa da tsaki suka bukaci Kwankwaso ya amince da shirinsu na zama a abokin takarar Obi a zaben shugaban kasa a 2027.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Matasa 3 Sun Shiga Hannu Kan Kashe Wani Mutum Don Mallakar Filinsa A Kano

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda kuma shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya ce yana jira ya ga ka’idojin da za a yi amfani da su wajen gudanar da irin wannan tsarin, duba da irin iliminsa da siyasa a kan Obi.

A wani faifan bidiyo da ya yi ta yawo a kafafen sada zumunta a ranar Asabar, an ga Kwankwaso na bayyana cewa, “Na fi Peter Obi girma a siyasance. Ni babban yayansa ne. Ina da kwarewa fiye da shi. Na yi kokari fiye da shi lokacin da nake gwamnan jihata.

“Ba ni da matsala wajen zama mataimakin takarar Peter Obi, amma sai dai idan an cika wasu sharudda,” in ji shi, yana mai jaddada cewa duk wani kawancen da za a iya kullawa dole ne a gina shi bisa amana.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya kara da cewa, “A shirye muke mu tattaunawa, muddin aka amince da sharuddanmu,” in ji shi, wanda ke nuna cewa shi da Obi a shirye suke su kulla kawancen siyasa da shugabancin jam’iyyar LP a gabanin zaben 2027.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi ne ya zo na uku a zaben da ya gabata da kuri’u 6,101,533, yayin da Kwankwaso ya taka rawar gani a jiharsa ta Kano, ya samu kuri’u 1,496,687 a kananan hukumomi 38 daga cikin 44 na jihar.

Kwankwaso ya kuma kasance mai sukar gwamnatin Shugaban kasa Bola Tinubu, musamman game da rabon kayan tallafin shinkafa a Jihar Kano. Ya zargi gwamnatin tarayya da kin bai wa gwamnatin jihar tallafin tare da mika wa ga ‘yan jam’iyyar adawa ta APC a jihar.

“Abun takaicin ne yadda gwamnatin tarayya ta raba tallafin shinkafa ga jihohi 35 a hannun gwamnoninsu, in ban da Jihar Kano wanda ak mika kason ga jiga-jigan APC. Wannan babban cin fuska ne ga dimokuradiyyar da kuma tsarin mulkinmu,” in ji Kwankwaso a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Tuwita.

Sai dai kuma, tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ya mayar wa da Kwankwaso martini, inda ya bayyana cewa Obi ne babba a siyasance fiye da Kwankwaso.

Ahmad, a cikin wani rubutu a shafinsa na Tuwita, ya ce duk da cewa ya kasance yana girmama Kwankwaso a matsayinsa na dan siyasa mai ci gaba, ba zai iya yin bara’a da furucin nasa ba.

Ya rubuta cewa, “Duk da cewa ban taba zama mai biyayya ga Kwankwasiyya ba, amma a ko da yaushe ina girmama Sanata Rabiu Kwankwaso kuma ina ganinsa a matsayin jiga-jigan dan siyasar da muke da su a kasar nan da ke samun ci gaba.

“Duk da haka, ban yarda da furucin da ya yi kwanan nan ba a lokacin da yake tattaunawa da shi a Kano, inda ya ce ya fi Peter Obi girma a siyasance. Idan aka dubi sakamakon zaben shugaban kasa na 2023, Peter Obi ya samu kuri’u 6,101,533 kuma ya yi nasara a jahohi 11, wanda ke nuna cewa ya samu goyon baya a kasatr nan. Sabanin yadda Sanata Kwankwaso ya samu kuri’u 1,496,687, wanda ya yi nasara a jiha daya kacal, Kano.

“Wadannan alkaluma sun nuna karara cewa, a kalla a yanayin zaben 2023, Peter Obi yana da matukar tasiri a siyasance a fadin kasar nan.

“Don haka Peter Obi ya fi Rabiu Kwankwaso girma a siyasance.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwankwasoObiSiyasatakara
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

7 days ago
Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

7 days ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

7 days ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.