• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarabar Taron Kolin G20

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarabar Taron Kolin G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tarihin duniya, kowane zamani kan gabatar da mafita ga matsalolinsa. Kazalika, bil Adama a yanzu yana fuskantar sabbin matsaloli, kamar tasirin sauyin yanayi, karancin wadatar albarkatun kasa, bala’in yunwa da har yanzu ke shafar mutane sama da miliyan 700 a duniya, babban rashin daidaiton kudin shiga tsakanin daidaikun mutane da kasashe, kwararowar masu kaura da matsalolin siyasa da na tattalin arziki da muhalli ke haifarwa, ga batun manyan laifuka na kasa da kasa, da habakar son kai da kariyar cinikayya a tsakanin kasashe masu arziki da ke illa ga manyan bukatun kasashe masu tasowa, duka wadannan matsaloli ne da ke addabar wannan zamani wadanda ke haifar da talauci da yunwa, kuma a kan su ne aka gina ajandar taron kolin G20 na bana.

 

A jiya Talata ne dai aka rufe taron kolin G20 wanda ya gudana a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil, taron da tashe-tashen hankula guda biyu masu muni, daya na Gabas ta Tsakiya da kuma na Ukraine suka karkatar da hankalin mahalarta daga muhimman batutuwan duniya kamar talauci da kawar da yunwa. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada matsayin kasar Sin wajen tabbatar da hadin kai don samar da duniya mai adalci da ci gaba tare yayin da shugabannin kasashen duniya na G20 suka yi alkawarin yin aiki tare a kan wadannan kalubalen da duniya ke fuskanta tare da amincewa da samar da mafitar dakatar da tashe-tashen hankula da ke kawo cikas ga zaman lafiyar duniya.

 

Shugaba Xi Jinping bai gaza sanar da matakai daban daban don bunkasa ci gaban duniya ba, inda ya jaddada goyon bayan da Beijing ke bayarwa ga ayyukan samar da ababen more rayuwa a duniya, da tsarin shawarar “Ziri daya da Hanya daya”, da shirin hadin gwiwar fasaha don tallafawa kasashe masu tasowa da shirin ci gaban duniya, da shirin samar da tsaro na duniya, da shirin wayewar kai na duniya, wadanda suka kasance gudummawar kasar Sin ga kasashen duniya don gina ayyukan da za su taimaka wajen shawo kan manyan kalubalen da bil Adama ke fuskanta. Mahalarta taron sun yi tsarabar ayyuka guda takwas da shugaba Xi ya gabatar don tallafawa ci gaban duniya. Yana mai cewa, “da taku daya ake fara tafiyar mil dubu,” kuma kasar Sin a shirye take ta dauki matakai tare da dukkan bangarori domin samar da duniya mai adalci ta hanyar samun ci gaba tare. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabannin Arewa Na Baya Sun Gaza – Uba Sani

Next Post

Kasar Sin: Ya Kamata Nahiyar Turai Ta Girmama Manufar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

10 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

11 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

12 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

13 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

14 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

15 hours ago
Next Post
Kasar Sin: Ya Kamata Nahiyar Turai Ta Girmama Manufar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Kasar Sin: Ya Kamata Nahiyar Turai Ta Girmama Manufar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.