• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Abokai, yanzu haka kasar Sin tana gudanar da babban taron wakilan jami’iyyar kwaminis da ke kan karagar mulkin kasar karo na 20, inda ake fatan gabatar da taswirar bunkasuwar Sin a nan gaba.

A rahoton da babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kana shugaban kasar Xi Jinping ya gabatar a gun taron, ya sake nanata muhimmancin gaggauta raya aikin noma. Yau “duniya a zanen MINA” zai bayyana muku muhimmancin tsarin zamanintar da aikin noma a Sin ga bunkasuwar duniya.

  • Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Injuna biyu na zamani da na zana, su ne babbar motar aikin gona maras matuki da karamin jirgin saman aikin gona maras matuki da Sin ta kera. Dukkansu na iya gudanar da aikin noma iri daban-daban ba tare da ma’aikata da dama ba.

Sin ta fito da wata managarciyar hanya da ta dace da halin da take ciki ta zamanintar da aikin noma bisa kimiyya da fasaha na zamani. Daga cikinsu, injunan aikin noma na zamani, ya ciyar da wannan aiki gaba.

Alkaluman kididdiga na nuna cewa, yawan kudaden dake shafar kasuwar sai dai injunan aikin noma, ya kai RMB Yuan biliyan 531, wanda ya karu da kashi 6.6% bisa makamancin lokaci na bara. Kana kasar tana fitar da injunan zuwa sassan duniya.

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Darektan cibiyar nazarin tsare-tsaren siyasa da tattalin arziki na kasar Armenia, mista Benjamin Pogo ya ce, rahoton da mista Xi Jinping ya gabatar a gun taron ya nuna cewa, kasar Sin ta gabatar da shawarar raya kasashen duniya da ma shawarar kiyaye tsaron duniya, wadanda take son aiwatarwa tare da kasa da kasa.

Ya ce, “Wadannan shawarwari sun bayyana fatan kasar Sin na cin moriya da samun bunkasuwa tare da ragowar kasashen duniya, kuma ya kasance babbar gudunmawar da ta bayar wajen magance kalubaloli da Bil Adama ke fuskanta, da ma ingiza ci gaban wayin kai da al’adun Bil Adama.”

A takaice, kasar Sin ta tsara managarciyar hanyar da ta dace da halin da take ciki na zamanintar da aikin noma bisa hanyoyi na kimiyya da fasahohi na zamani. Ban da wannan kuma, manufar bude kofa ga kasashen ketare da take aiwatarwa na taimakawa wajen fitar da wadannan injuna da fasahohi zuwa ketare.

Bunkasuwar al’umma ta ta’allaka da tsaron hatsi, kuma tabbatar da samar da isashen hatsi na da babbar ma’ana ga raya kasa mai wadata.

Ko shakka babu, bisa shawarar raya duniya baki daya, yadda kasar Sin ke zamanintar da aikin noma zai samar da gudummawarta wajen warware matsalar karancin hatsi da raya aikin gona, matakin da ko shakka babu, zai baiwa duniya kwarin gwiwa da kuzari wajen tabbatar da samun bunkasuwa. (Mai zane da rubuta: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Kashe ‘Yan Ta’addar Da Suka Addabi Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

Jami'an Tsaro Sun Kashe 'Yan Ta'addar Da Suka Addabi Mutane A Hanyar Abuja-Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.