• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsige McCarthy Daga Mukaminsa Ya Nuna Me Ake Nufi Da “Dimokradiyyar Amurka”

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
McCarthy
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 3 ga watan Oktoba, ‘yan majalisar wakilai da ke karkashin jagorancin jam’iyyar Republican, suka kada kuri’u 216 na amincewa da 210 na kin amincewa don tsige kakakin majalisar Kevin McCarthy daga mukaminsa.

A ranar 1 ga watan Oktoban kowace shekara ne a kan fara gudanar da kasafin kudin gwamnatin tarayyar Amurka.

  • ‘Yan Jarida Sun Yaba Da Ci Gaba Da Al’adun Jihar Xinjiang
  • Gazawar Manyan Kasashe Na Biyan Kudin Memba Ya Sa MDD Ke Fuskantar Karancin Kudaden Gudanarwa

Tun daga watan Satumbar bana, takaddamar da ke tsakanin jam’iyyun siyasa biyu a Amurka game da kasafin kudin sabuwar shekara ke kara kamari. A ranar 30 ga wata, a matsayinsa na kakakin majalisar wakilai, McCarthy ya yanke shawarar hada kai da ‘yan jam’iyyar Democrat, don zartar da kudurin bayar da kudi na wucin gadi. Bugu da kari, kudurin bai hada da shawarwarin masu ra’ayin rikau na jam’iyyar Republican ba, na rage yawan kudin da gwamnatin tarayya ke kashewa da kuma tsaurara matakan kula da iyakokin kasa. Hakan ya kara rura wutar rikicin da ke tsakaninsa da masu ra’ayin rikau a jam’iyyar Republican.

A daren ranar 2 ga watan Oktoban, dan Republican mai ra’ayin rikau wato Matt Gaetz, ya gabatar da kudurin tsige Kevin McCarthy, bisa dalilin dake cewa “Yana hidimtawa jam’iyyar Democrat.”
Jam’iyyar Republican tana da kujeru 221 a majalisar wakilai, wanda ya zarce kujeru 212 na jam’iyyar Democrat. Duk da haka, saboda “tawayen” wasu ‘yan majalisar Republican takwas masu ra’ayin rikau, daga karshe majalisar ta tsige McCarthy.

Kamar yadda manazarta da dama suka yi nuni, adawar da ake yi tsakanin jam’iyyun siyasa a Amurka da kuma yadda ake gwabza fada tsakanin jam’iyyun na daga cikin muhimman dalilan da suka saukar da McCarthy daga mukaminsa. Saboda rikicin jam’iyyun, wasu mambobi masu ra’ayin rikau kadan na iya yin tasiri a kan zaben shugaban majalisar wakilai, wannan alama ce da ke nuna yanayin siyasar Amurka a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Wannan lokacin ne da siyasar Amurka ta yi amfani da muradun son kai na wasu tsirarun mutane, kuma lokaci ne da aka mayar da dimokuradiyyar Amurka matsayin “wasan mulki,” to ta yaya za a iya amincewa da “labarin dimokuradiyya” da ‘yan siyasar Amurka suka rubuta? (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenPutin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Next Post

Argentina Ta Gayyaci Messi Buga Mata Wasa Duk Da Raunin Da Ya Samu

Related

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

2 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

3 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

4 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

5 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

1 day ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Messi

Argentina Ta Gayyaci Messi Buga Mata Wasa Duk Da Raunin Da Ya Samu

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.