• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsige McCarthy Daga Mukaminsa Ya Nuna Me Ake Nufi Da “Dimokradiyyar Amurka”

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
McCarthy
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 3 ga watan Oktoba, ‘yan majalisar wakilai da ke karkashin jagorancin jam’iyyar Republican, suka kada kuri’u 216 na amincewa da 210 na kin amincewa don tsige kakakin majalisar Kevin McCarthy daga mukaminsa.

A ranar 1 ga watan Oktoban kowace shekara ne a kan fara gudanar da kasafin kudin gwamnatin tarayyar Amurka.

  • ‘Yan Jarida Sun Yaba Da Ci Gaba Da Al’adun Jihar Xinjiang
  • Gazawar Manyan Kasashe Na Biyan Kudin Memba Ya Sa MDD Ke Fuskantar Karancin Kudaden Gudanarwa

Tun daga watan Satumbar bana, takaddamar da ke tsakanin jam’iyyun siyasa biyu a Amurka game da kasafin kudin sabuwar shekara ke kara kamari. A ranar 30 ga wata, a matsayinsa na kakakin majalisar wakilai, McCarthy ya yanke shawarar hada kai da ‘yan jam’iyyar Democrat, don zartar da kudurin bayar da kudi na wucin gadi. Bugu da kari, kudurin bai hada da shawarwarin masu ra’ayin rikau na jam’iyyar Republican ba, na rage yawan kudin da gwamnatin tarayya ke kashewa da kuma tsaurara matakan kula da iyakokin kasa. Hakan ya kara rura wutar rikicin da ke tsakaninsa da masu ra’ayin rikau a jam’iyyar Republican.

A daren ranar 2 ga watan Oktoban, dan Republican mai ra’ayin rikau wato Matt Gaetz, ya gabatar da kudurin tsige Kevin McCarthy, bisa dalilin dake cewa “Yana hidimtawa jam’iyyar Democrat.”
Jam’iyyar Republican tana da kujeru 221 a majalisar wakilai, wanda ya zarce kujeru 212 na jam’iyyar Democrat. Duk da haka, saboda “tawayen” wasu ‘yan majalisar Republican takwas masu ra’ayin rikau, daga karshe majalisar ta tsige McCarthy.

Kamar yadda manazarta da dama suka yi nuni, adawar da ake yi tsakanin jam’iyyun siyasa a Amurka da kuma yadda ake gwabza fada tsakanin jam’iyyun na daga cikin muhimman dalilan da suka saukar da McCarthy daga mukaminsa. Saboda rikicin jam’iyyun, wasu mambobi masu ra’ayin rikau kadan na iya yin tasiri a kan zaben shugaban majalisar wakilai, wannan alama ce da ke nuna yanayin siyasar Amurka a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

Wannan lokacin ne da siyasar Amurka ta yi amfani da muradun son kai na wasu tsirarun mutane, kuma lokaci ne da aka mayar da dimokuradiyyar Amurka matsayin “wasan mulki,” to ta yaya za a iya amincewa da “labarin dimokuradiyya” da ‘yan siyasar Amurka suka rubuta? (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenPutin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Nasiru A Kebbi

Next Post

Argentina Ta Gayyaci Messi Buga Mata Wasa Duk Da Raunin Da Ya Samu

Related

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya
Daga Birnin Sin

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

16 hours ago
Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Bunkasa Cinikayyar Ayyukan Hidimomi Masu Inganci

17 hours ago
Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi
Daga Birnin Sin

Adadin Cinikayyar Sin Da Kasashen Kungiyar SCO Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

20 hours ago
Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Jimilar Darajar Hada-Hadar Shige Da Fice A Fannin Bayar Da Hidimomi Ta Kasar Sin Ta Kai Yuan Tiriliyan 3.9 A Rabin Farko Na Shekarar Bana

20 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

22 hours ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

22 hours ago
Next Post
Messi

Argentina Ta Gayyaci Messi Buga Mata Wasa Duk Da Raunin Da Ya Samu

LABARAI MASU NASABA

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

August 28, 2025
Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

Tallafin Walwalar Jama’a: Yadda Gwamnatocin Biranen Kasar Sin Ke Jifan Tsuntsu Biyu Da Dutse Daya

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.