• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turjewa Kariyar Cinikayya Na Nufin Ingantaciyyar Alkibla Mai Dorewa

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Cinikayya

Matakan kariyar cinikayya daga wasu kasashe masu ci gaba wadanda ke cin karo da yunkurin dunkulewar tattalin arzikin duniya ba su taba sanyaya gwiwar kasar Sin wajen kara karfafa huldar cinikayya tsakaninta da kasashe masu huldar diflomasiyya da ita ba. Daga cikin matakan baya bayan nan da kasar Sin ta dauka wajen dunkulewar tattalin arzikin duniya shi ne kasashe masu karamin karfi da ke da huldar diflomasiyya da ita za su ci gajiyar soke haraji kan kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasar Sin. Wannan matakin ya nuna aniyar kasar Sin na tabbatar da ra’ayin bangarori daban daban, da goyon bayan cinikayya mara shinge a cikin yanayin kasa da kasa mai sarkakiya, da kuma sauke nauyin da ke wuyanta a matsayinta na babbar kasa.

 

Kana kasancewar kasar Sin kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki, kuma kasa mafi karfi da girma a fannin cinikayyar kayayyaki, shawarwarin tattalin arziki da manufofinta na cinikayya suna da tasiri mai matukar muhimmanci. Duk da yanayin da ake ciki na yaki da kariyar cinikayya a duniya, kasar Sin ta ci gaba da bude kofa ga kasashen duniya, da ci gaba da aiwatar da matakai da shawarwarin bangarori daban daban kan yin ciniki cikin ‘yanci, da ci gaba da ingiza farfadowar tattalin arzikin duniya. Wannan ba wai kawai yana taimakawa wajen tabbatar da cinikayya cikin lumana da kyautata tafiyar da tsarin masana’antun duniya da tsarin samar da kayayyaki ba, har ma yana samar da damammakin kasuwanci ga kamfanoni daga kasashe daban daban da kuma samar da mafi kyawun kason albarkatun duniya. Bugu da kari, A matsayinta na kasa mai tasowa, kasar Sin ta fahimci wahalhalun dake tattare da yunkurin neman ci gaba, kuma a ko da yaushe tana amfani da sanin ya kamata, tare da kokarin samun ci gaba kafada da kafada da sauran kasashe masu tasowa.

 

Muna iya ganin yadda habakar shingen kasuwanci ya sa yanayin kasuwancin duniya cikin tangal tangal, kuma bunkasar tattalin arzikin duniya na fuskantar babban matsi, don haka manufar soke haraji kan kayayyakin kasashe mara sa karfi dake shigowa kasar Sin ta ingiza fatar farfadowar tattalin arzikin duniya. Kuma ko shakka babu kasar Sin za ta ci gaba da bin hanyar samun ci gaba ba tare da wata matsala ba, tare da yin aiki da kasashen duniya don tinkarar kalubalen da duniya ke fuskanta, da ba da gudummawa sosai wajen bunkasa tattalin arzikin duniya, da tabbatar da burin ci gaban bil Adama ta bai daya. Da fatan sauran kasashe za su bi sahun kasar Sin, da daukar matakan turjewa kariyar cinikayya, da kuma tafiyar da tattalin arzikin duniya zuwa ga samun ingantacciyar alkibla mai dorewa. (Mohammed Baba Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia
Daga Birnin Sin

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Next Post
CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.