• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ukraine Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniya Kan Ma’adanai – Jami’in Ukraine

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
in Kasashen Ketare
0
Ukraine Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniya Kan Ma’adanai – Jami’in Ukraine
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ukraine da Amurka sun cimma matsaya kan tsarin kulla yarjejeniyar tattalin arziki mai fadi da za ta hada da samun damar mallakar ma’adanan karkashin kasa da babu su a duniya, in ji wasu manyan jami’ain Ukraine uku.

Jami’an, wadanda ke da masaniya kan lamarin, sun yi magana bisa sharadin a sakaya sunayensu saboda ba’a ba su izinin magana a bainar jama’a ba.

  • Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya
  • CBN Ya Umarci Daraktocin Bankuna Su Mayar Da Bashin Da Suka Karba Ko Su Yi Murabus

Daya daga cikinsu ya ce Kyib na fatan sanya hannun kan yarjejeniyar don tabbatar da ci gaba da bayar da tallafin sojin Amurka da Ukraine ke bukata cikin gaggawa.

Da yake magana da manema labarai a ofishin shugaban kasa, Donald Trump, ya ce ya ji cewa Zelenskyy na zuwa, ya kuma kara da cewa “babu komai a wurina, idan ya so, kuma yana iya sanya hannun tare da ni.”

Za’a iya sanya hannun kan yarjejeniyar nan da ranar Juma’a mai zuwa kuma an shirya tsaf game da tafiyar shugaban Ukraine Bolodymyr zuwa Washington don ganawa da Trump, a cewar daya daga cikin jami’in Ukraine.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9

Trump: Yadda Sabuwar Dokar Hana Shiga Amurka Ta Fi Shafar Musulmai Da Afirka

Wani jami’in ya ce yarjejejeniyar za ta ba da dama ga Zelenskyy da Trump su tattauna batun ci gaba da bayar da tallafin soji ga Ukraine, dalilin da ya sa Kyib ke son kammala yarjejeniyar.

Trump ya kwatanta wannan matsaya da aka cimma a matsayin “babbar yarjejeniyar,” wacce za ta kai ta tiriliyan na daloli.

A wani labarin kuma, Kasar Ukraine ta bayyana cewar hare-haren da Rasha ta kai wa garuruwan dake kusa da filin daga a gabashin kasar sun hallaka akalla mutum 5 tare da raunata wasu 8 ‘yan sa’o’i bayan wani mummunana harin jirgi mara matuki kusa da birnin Kyib.

Gagarumin ruwan wutar da jiragen saman Rasha marasa matuka suka kai cikin dare sun hallaka mutum 2 a kusa da birnin Kyib, ciki har da wata ‘yar jaridar Ukraine, kamar yadda kafar yada labaran da take yiwa aiki ta bayyana.

‘Yan jaridar dake yi wa kamfanin dillancin labarai na Afp aiki a Kyib sun ji karar fashewa bayan da rundunar sojin saman Ukraine ta ce Rasha ta yi barin wuta da jirage sama marasa matuka 177 masu nau’uka daban-daban kan wuraren da ta kai wa hari a fadin kasar.

Dakarun Rasha na kokarin kwace iko da garin Kostyantynibka kuma sun tsananta wajen yin luguden wuta akan sansanonin farar hula dake yankin gabashin Donetsk, wanda fadar Kremlin ke ikrarin cewa wani bangare ne na Rasha.

“An hallaka akalla mutum 5 kana an raunata wasu 8 a hare-haren da ake kai wa Kostyantynibka,” kamar yadda gwamnan yankin Donetsk Badim Filashkin ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Hare-haren wata shaida ce ga karin wahalar da dakarun Ukraine ke sha a hannun rundunar sojin Rasha wacce ta ninkasu kudi da kayan aiki da kuma yawan dakaru a fadin fagagen daga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaTrumpUkraineZelensky
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saudiyya Ta Raba Tan Hamsin Na Dabino A Nijeriya

Next Post

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Related

Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
Kasashen Ketare

Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9

3 days ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

Trump: Yadda Sabuwar Dokar Hana Shiga Amurka Ta Fi Shafar Musulmai Da Afirka

5 days ago
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa
Kasashen Ketare

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

1 week ago
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta
Kasashen Ketare

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

3 weeks ago
Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 
Kasashen Ketare

Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci
Kasashen Ketare

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

4 weeks ago
Next Post
Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 14, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

June 14, 2025
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

June 14, 2025
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

June 14, 2025
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

June 14, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.