• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ukraine Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniya Kan Ma’adanai – Jami’in Ukraine

by Rabi'u Ali Indabawa
5 months ago
in Kasashen Ketare
0
Ukraine Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniya Kan Ma’adanai – Jami’in Ukraine
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ukraine da Amurka sun cimma matsaya kan tsarin kulla yarjejeniyar tattalin arziki mai fadi da za ta hada da samun damar mallakar ma’adanan karkashin kasa da babu su a duniya, in ji wasu manyan jami’ain Ukraine uku.

Jami’an, wadanda ke da masaniya kan lamarin, sun yi magana bisa sharadin a sakaya sunayensu saboda ba’a ba su izinin magana a bainar jama’a ba.

  • Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya
  • CBN Ya Umarci Daraktocin Bankuna Su Mayar Da Bashin Da Suka Karba Ko Su Yi Murabus

Daya daga cikinsu ya ce Kyib na fatan sanya hannun kan yarjejeniyar don tabbatar da ci gaba da bayar da tallafin sojin Amurka da Ukraine ke bukata cikin gaggawa.

Da yake magana da manema labarai a ofishin shugaban kasa, Donald Trump, ya ce ya ji cewa Zelenskyy na zuwa, ya kuma kara da cewa “babu komai a wurina, idan ya so, kuma yana iya sanya hannun tare da ni.”

Za’a iya sanya hannun kan yarjejeniyar nan da ranar Juma’a mai zuwa kuma an shirya tsaf game da tafiyar shugaban Ukraine Bolodymyr zuwa Washington don ganawa da Trump, a cewar daya daga cikin jami’in Ukraine.

Labarai Masu Nasaba

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

Wani jami’in ya ce yarjejejeniyar za ta ba da dama ga Zelenskyy da Trump su tattauna batun ci gaba da bayar da tallafin soji ga Ukraine, dalilin da ya sa Kyib ke son kammala yarjejeniyar.

Trump ya kwatanta wannan matsaya da aka cimma a matsayin “babbar yarjejeniyar,” wacce za ta kai ta tiriliyan na daloli.

A wani labarin kuma, Kasar Ukraine ta bayyana cewar hare-haren da Rasha ta kai wa garuruwan dake kusa da filin daga a gabashin kasar sun hallaka akalla mutum 5 tare da raunata wasu 8 ‘yan sa’o’i bayan wani mummunana harin jirgi mara matuki kusa da birnin Kyib.

Gagarumin ruwan wutar da jiragen saman Rasha marasa matuka suka kai cikin dare sun hallaka mutum 2 a kusa da birnin Kyib, ciki har da wata ‘yar jaridar Ukraine, kamar yadda kafar yada labaran da take yiwa aiki ta bayyana.

‘Yan jaridar dake yi wa kamfanin dillancin labarai na Afp aiki a Kyib sun ji karar fashewa bayan da rundunar sojin saman Ukraine ta ce Rasha ta yi barin wuta da jirage sama marasa matuka 177 masu nau’uka daban-daban kan wuraren da ta kai wa hari a fadin kasar.

Dakarun Rasha na kokarin kwace iko da garin Kostyantynibka kuma sun tsananta wajen yin luguden wuta akan sansanonin farar hula dake yankin gabashin Donetsk, wanda fadar Kremlin ke ikrarin cewa wani bangare ne na Rasha.

“An hallaka akalla mutum 5 kana an raunata wasu 8 a hare-haren da ake kai wa Kostyantynibka,” kamar yadda gwamnan yankin Donetsk Badim Filashkin ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Hare-haren wata shaida ce ga karin wahalar da dakarun Ukraine ke sha a hannun rundunar sojin Rasha wacce ta ninkasu kudi da kayan aiki da kuma yawan dakaru a fadin fagagen daga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaTrumpUkraineZelensky
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saudiyya Ta Raba Tan Hamsin Na Dabino A Nijeriya

Next Post

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Related

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

5 days ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

6 days ago
Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

2 weeks ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

2 weeks ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

2 weeks ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

2 weeks ago
Next Post
Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan Betis

LABARAI MASU NASABA

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

July 26, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.