• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

WAFU 2025: Gwamnatin Tarayya Ta Yabi Super Falcons a Matsayin Zakarun Afrika

bySulaiman
2 months ago
Wafu

Gwamnatin Tarayya a yau ta shirya kyakkyawar tarba ga ‘yan ƙwallon mata, wato Super Falcons, bayan dawowar su daga Rabat, babban birnin ƙasar Morokko, inda suka lashe gasar Kofin Afrika na Mata ta CAF ta shekarar 2024 a matsayin zakarun Afrika.

A cikin wata sanarwa, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana nasarar a matsayin fiye da cin gasar wasanni kawai, yana mai cewa, “nasarar wata shaida ce ta jajircewa, ƙwazo, da ƙarfin gwiwar ‘yan Nijeriya wadda Super Falcons ta nuna.”

  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

Da yake jawabi a madadin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnatin Tarayya, Ministan ya yaba wa ‘yan wasa, da masu horaswa da tawagar ma’aikatan su bisa jajircewar su da sadaukarwar su.

Ya ce: “Kun zamo abin koyi ga matasa a Nijeriya, kuma kun nuna irin tasirin da wasanni suke da shi wajen haɗa kan jama’a da kuma ƙarfafa gwiwa.”

Ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu tana da cikakken ƙudiri wajen ci gaba da saka jari a fannin wasanni da tallafa wa ‘yan wasa, ta hanyar samar da ababen more rayuwa da matakan da za su ba su damar yin fice.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Yayin da Super Falcons ke shigowa Abuja, ministan ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su fito su tarbi ƙungiyar a lokacin tafiyar da za su yi daga ƙofar birnin Abuja zuwa Dandalin Eagle har zuwa Fadar Shugaban Ƙasa, inda za a karɓe su a hukumance.

“Super Falcons sun ɗaga tutar Nijeriya sama, sun kuma kawo farin ciki ga miliyoyin ‘yan ƙasa. Barkan ku da dawowa, zakarun Afrika!” inji shi.

A ranar Asabar dai Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Super Falcons ɗin murna kan nasarar da suka samu a gasar.

A takardar sanarwa wadda Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai, Mista Bayo Onanuga, ya rattaba wa hannu, Tinubu ya ce, “Gagarumar nasarar da Super Falcons suka samu a daren yau a Rabat, inda suka zo daga ‘yan sahun baya suka buge Marokko da ke da ƙarfi kuma a gaban ‘yan kallo masu shauƙi, alama ce ta jan halin da ‘yan Nijeriya suke da shi.

“Tare da aiki tukuru, sadaukarwa da jajircewar, kun cimma nasarar da ƙasar nan take fatan samu kuma take addu’a a kai. Ƙasar nan tana sa ran yin kyakkyawar tarba ga gwarzayen mu. Muna murna! Nijeriya tana ɗokin ku.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version