• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwayen Kanun Manyan Labarai

by Ishaq Idris Gulbi
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Waiwayen Kanun Manyan Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu Alaikum barkanmu da asubahin Asabar, shida ga watan Safar, shekarar 1444 bayan hijirar cikamakin annabawa kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad S. A. W.

Daidai da uku ga watan Satumba, shekarar 2022. Da fatan yau za a gafarce ni saboda matsala ta wutar lantarki ban iya kalato muku labari ko daya ba.

  • ‘Yan Takarar Jihar Kano Sun Gamsu Da Taron KJPF
  • Za A Yi Zaman Makokin Elizabeth Na Kwanaki 7 Da Binne Ta

A ‘yan kwanakin nan wutar sai ci gaba da tabarbarewa take yi. A yini da kyar a samu wutar minti talatin.

Talaka zai ci gaba da biyan kudin zama a duhu a zamanin mulkin masu gaskiya. Ga Hamid Ali ma ya ce damfarar talakan Nijeriya ake yi da ake cewa wai ana biyan kudin tallafin mai. Ga ‘ya’yan talaka da suke karatu a jami’a wata shida suna gida ba karatu.

LAHADI

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Gwamnatin Tarayya ta nanata cewa no work no pay ga malaman jami’a da ke yajin aiki. Wata dai na bakwai ke nan da gwamnati ta dakatar da albashin malaman da ke yajin aikin. Malaman sun ce ba gudu ba ja da baya.

Yajin aiki ya ci gaba. Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da wani rumbun tattara bayanai da adana su, na dukkan wanda wata hukuma ta tsaro ta kama.

Hukumomin ‘yan sanda suna nan suna bincikar wani dan sanda, da ake zargin ya nemi ya yi lalata da wata budurwa mai shekara 17 da aka tsare ta a ofishin ‘yan sanda.

Gwamnatin Tarayya, ta kara wa ministoci da manyan sakatarori da sauransu, yawan kudin alawus na tafiye-tafiye.

Hukumomin soja, sun bullo da wata horarwa ta soja ta dole ta mako shida, ga yara da suka kammala makarantar ‘ya’yan sojoji da aka fi sani da Military School.

Kotu ta wanke tsohon gwamnan Jihar Filato Jonah Jang, daga zargin da ake masa na ya wawuri wata Naira Biliyan shida da kusan rabi.

A Jihar Zamfara masu fashin jama’a sun yi fashin liman da masallata masu yawan gaske a lokacin sallar Jumu’a.

A Jihar Katsina masu fashin jama’a, sun je rugar fulani, suka yi fashin fulani da dabbobinsu. Haka nan masu bin jama’a har gida su yi fashinsu sun addabi mutanen Funtuwa.

Kungiyar Makira Waya ta Jihar Kaduna, za ta gudanar da wani babban taronta a Lahadin nan a Kaduna, inda aka gayyaci malamanmu da mu dalibai, mu gabatar da makaloli. Tawa makalar ita ce Dangantakar Makira Waya Da Kafofin Watsa Labaru.

LITININ

Shugaban Hukumar Kwastam Hamid Ali, ya sake jaddada cewa duk wani batu da ake yi na cewa ana tallafi ga man fetur, damfara ce kawai ake yi, take karewa a kan tallaka.

Kungiyar SERAP mai rajin kare hakkin talaka, ta nemi shugaban kasa Buhari, ya janye sunayen mutanen da ya aike wa Majalisar Dattawa ta amince da su a matsayin kwamishinonin zabe, wadanda ‘yan jam’iyyar APC ne, domin ba za su yi adalci ba a zabukan shekara mai zuwa.

Shugaban ‘yan sandan Nijeriya, ya ba da tabbacin babu wata barazana da za ta hana gudanar da zabukan shekara mai zuwa.

A wata daya kacal, Nijeriya ta samu gibin kudi Naira Biliyan 524 da ‘yan kai.

‘Yan Boko Haram sun kutsa wani masallaci suka kashe limamin da ke limancin sallah da sauran masallata da ke bin limamin sallah a Jihar Barno.

Ambaliya tana neman raba Jihar Gwambe da sauran jihohi da take makwabtaka da su. Wadanda suka yi fashin wani shugaban gundumar raya kasa a Jihar Zamfara, sun masa kudi Naira Miliyan Ashirin.

Makarantar horar da kananan hafsoshin ‘yan sanda da ke Wudil, ta koka a game da yadda jaridar Sahara Reporters, ta tasa makarantar a gaba tana neman sai ta ga bayanta.

A Jihar Kaduna, an kama masu yi wa mutane cinne ga masu fashin jama’a a unguwa, su uku da aka fi sani da INFORMANTS a yankin karamar hukumar Igabi.

TALATA

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya ba da umarnin dakatar da yunkurin da ake yi na karin kudin kiran waya.

Lai da Magashi, sun ce kwanan matsalar tabarbarewar tsaro a Nijeriya ya kare sai dai uwarta ta haifi wata.

Gwamnatin Tarayya, ta kwace wasu kaddarori goma sha hudu, da suke da nasaba da dakataccen dan sanda Abba Kyari, ta kuma tsara tuhume-tuhume kusan 24 da take masa.

Yau ministan ilimi da shugabannin jami’o’i da iyayen jami’o’i da hukumomin gudanarwa na jami’o’i, za su taru domin tattauna yajin aikin da malaman jami’a suke kan yi.

A dai Jihar Kaduna, mahukuntan jami’ar Jihar Kaduna, sun ba malaman jami’ar zuwa jiya, ko su koma aiki, ko malaman su gani a kwaryar cin su ko ta shan su.

Kamfanin mai na kasa NNPC, ya ce Allah kuwa da gaske ne a kullum ana shan man fetur lita miliyan sittin da takwas a kasar nan.

A ta daya bangaren kuma da alamu za a kuma aukawa matsalar man fetur saboda dillalan man na shirin daka barkono su yi yaji.

Ana ta yabon kwamishinan tsara birane da raya su na Jihar Legas Idris, saboda sauka da ya yi daga kan mukaminsa, saboda rushewar da wani bene da ake kan gina shi a Lekki ya yi da zuwa yanzun an ciro gawar mutum shida daga baraguzan ginin.

Mutanen yankin Kinkinau da na Unguwar Mu’azu da ke cikin garin Kaduna, sun yaba wa dan takaran majalisar dokoki ta Jihar Kaduna na jam’iyyar APGA na mazabar Tudun Wadar Kaduna, Aminu Soja Gida Gida, saboda kokarin da yake yi bangaren tsaro har ya kafa JTF ta Unguwar Mu’azu da Kinkinau.

Ya kuma koya wa yara da mata sana’o’i na dogaro da kai, da ci gaba da taimaka wa marasa galihu.

Sojoji sun kashe kwamandojin ISWAP da Boko Haram su biyar, da mayakansu fiye da dari biyu a Jihar Barno.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Manyan LabaraiWaiwaye
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ceto Mutane Fiye Da 650 Da Girgizar Kasa Da Ta Auku A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

Next Post

An Mika Cibiyar Wasannin Motsa jiki Da Al’adu Da Kasar Sin Ta Samarwa Tunisia

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

2 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

7 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

11 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

12 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
An Mika Cibiyar Wasannin Motsa jiki Da Al’adu Da Kasar Sin Ta Samarwa Tunisia

An Mika Cibiyar Wasannin Motsa jiki Da Al'adu Da Kasar Sin Ta Samarwa Tunisia

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.