• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Don Tinkarar Barazanar Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wajen taron yaki da ta’addanci da kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya shirya a jiya Alhamis 15 ga wata, wakilin dindindin na kasar Sin dake majalisar, Zhang Jun ya jaddada muhimmancin karfafa hadin-gwiwa domin yakar barazanar ta’addanci, inda kuma ya yi kira da a murkushe duk wani nau’in ta’addanci, da zummar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Jami’in ya ce, ta’azzarar rikicin Palesdinu da Isra’ila ya janyo karin munanan laifuffukan nuna kiyayya da aka aikata a kasashe daban-daban, kuma ana kara fuskantar barazanar hare-haren ta’addanci. Abun dake gaban komai a halin yanzu shi ne, tsagaita bude wuta a zirin Gaza, don kar halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya ya ci gaba da tabarbarewa.

  • Xi Ya Taya Stubb Murnar Zabarsa A Matsayin Shugaban Finland
  • Dokar Hana Fitar Da Kayan Gini Waje: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Motoci 5 Makare Da Siminti A Adamawa

Jami’in ya kuma ce, yankin yammacin Afirka da na Sahel na fuskantar babbar barazanar hare-haren ta’addanci, kuma babban dalilin da ya sa haka shi ne rashin kwarewa wajen murkushe su. Don haka ya zama dole MDD da sauran kasashen duniya su yi la’akari da bukatun kasashen Afirka, da kara ba su taimako.

Ha wa yau, jami’in ya ce, har kullum kasar Sin tana maida hankali sosai wajen halartar hadin-gwiwar kasa da kasa a fannin yaki da ta’addanci. Kwanan nan ne kasar ta bullo da takardar bayani kan tsarin doka da matakan yaki da ta’addanci, inda aka takaita muhimman ayyuka gami da nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin yakar ta’addanci. Kuma a nan gaba, Sin za ta ci gaba da inganta hadin-gwiwa tare da sauran kasashe, domin aiwatar da shawarar kiyaye tsaro a duniya da shugaban kasar ya bullo da ita. (Murtala Zhang)

 

Labarai Masu Nasaba

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Tabarbare A Cikin Shekara 10

Next Post

An Bukaci Tinubu Ya Nemi Kasashen Turai Su Yafe Wa Nijeriya Basukanta

Related

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

53 minutes ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

2 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

3 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

4 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

6 hours ago
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

24 hours ago
Next Post
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

An Bukaci Tinubu Ya Nemi Kasashen Turai Su Yafe Wa Nijeriya Basukanta

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.