• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin: Ya Kamata Kasashen Duniya Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Shawo Kan Kalubale Tare

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Dai Bing, ya yi jawabi karkashin ajandar babban taron MDD karo na 78, bisa taken “Karfafa hadin gwiwar taimakon jin kai da rage radadin bala’o’i na MDD”, inda ya yi kira ga kasashen duniya da su karfafa hadin kai da hadin gwiwa, da yin aiki tare don taimakawa kasashen da ke fama da matsalar jin kai su shawo kan matsaloli da kalubale.

Dai Bing ya ce, kimanin mutane miliyan 364 a fadin duniya ne ke bukatar agajin jin kai, kuma yawan kudin da ake bukata don ba da agajin jin kai ta kai dalar Amurka biliyan 55.9, amma masu ba da agaji sun ba da dalar Amurka biliyan 18.3 kawai, wanda ya kai kashi 32.7 bisa 100 na adadin abin da ake bukata. Kasashen da suka ci gaba, a matsayinsu na manyan masu bayar da agajin jin kai, wadanda ke da alhakin tarihi, ya kamata su cika alkawurran da suka yi wajen bayar da gudummawar a kan lokaci da cika alkawurran bayar da agajin da kuma cike gibin tallafin jin kai yadda ya kamata.

  • Tsohon Firaministan Austria: Ra’ayin “Raba Gari Ta Fannin Tattalin Arziki” Bai Dace Ba
  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya

Dai Bing ya kara da cewa, tun bayan barkewar rikicin Palasdinawa na Isra’ila, a halin yanzu al’ummar Palasdinawa musamman mata da kananan yara a yankin zirin Gaza, na fuskantar hasarar rayuka baya ga raba su da muhallansu. Yanayin zamantakewa da tattalin arziki ya ruguje, kana abubuwan more rayuwa sun lalace matuka. Mutane fiye da miliyan 2 a zirin Gaza na cikin mawuyacin hali. Don haka ya kamata al’ummomin kasa da kasa, su inganta tsagaita bude wuta mai dorewa da daukar managartan matakai don kare rayukan fararen hula, musamman mata da kananan yara, da hanzarta dawo da ayyukan jin kai.

Ya bayyana cewa, kasar Sin ta kasance mai kiyaye zaman lafiya a duniya, kuma mai sa kaimi ga samun ci gaba tare, da himmantuwa wajen inganta aikin gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil-Adama. (Ibrahim)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Next Post
Yawan Yaran Da Ke Fama Da Cututtuka Masu Alaka Da Sassan Jiki Masu Taimakawa Numfashi Ya Ragu A Kasar Sin

Yawan Yaran Da Ke Fama Da Cututtuka Masu Alaka Da Sassan Jiki Masu Taimakawa Numfashi Ya Ragu A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Sin

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.