• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

by CGTN Hausa
2 years ago
Kongo

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Bisa gayyatar da shugaba Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo na Jamhuriyar Demokaradiyyar Kongo ya yi mata, wakiliyar musamman ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana mataimakiyar shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin Shen Yueyue, ta halarci bikin rantsar da shugaban kasar a Kinshasa, babban birnin jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a ranar 20 ga watan Janairu. A jiya Lahadi ranar 21 ga wata kuma, shugaba Tshisekedi ya gana da madam Shen Yueyue a Kinshasa.

A yayin ganawarsu, madam Shen Yueyue ta isar da sakon gaisuwa da fatan alheri da shugaba Xi Jinping ya yi ga Tshisekedi. Tana mai cewa, kasar Sin na mai da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Kongo Kinshasa, kuma a shirye take ta yi aiki tare da Kongo Kinshasa wajen aiwatar da muhimman ra’ayoyin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da nuna goyon baya ga juna kan muhimman muradunsu, da zurfafa hadin gwiwa irin na samun moriyar juna da cin nasara tare, da kuma ciyar da sada zumunta a tsakanin jama’ar kasashen biyu, kana da zurfafa yin mu’amala da hadin gwiwa bisa tsarin raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” da na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wato FOCAC, da nufin karfafa kyakkyawar dangantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen Sin da Kongo Kinshasa.

A nasa bangaren, Tshisekedi ya mika godiyarsa ga shugaba Xi Jinping bisa aiko da wakiliya ta musamman don halartar bikin rantsar da shi, ya kuma bukaci Shen Yueyue da ta mika sakon gaisuwa da fatan alheri ga shugaba Xi Jinping. Baya ga haka, Tshisekedi ya jinjina sosai ga ci gaban da aka samu a cikin shirin hadin gwiwa na RFI, wato amfani da ayyukan habaka albarkatu don inganta ayyukan samar da ababen more rayuwa a tsakanin Kongo Kinshasa da Sin. Haka zalika ya bayyana cewa, kasarsa tana mai da hankali sosai kan dadadden zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, tana mai bin manufar Sin daya tak, da kuma fatan zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a wasu muhimman fannoni, ciki har da hakar ma’adinai da dai sauransu, don sa kaimi ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta kai wani sabon matsayi. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Tinubu

Gwamnatin Tarayya Ta shirya Kaddamar Da Shirin Baiwa Dalibai Bashi 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.