• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Bisa gayyatar da shugaba Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo na Jamhuriyar Demokaradiyyar Kongo ya yi mata, wakiliyar musamman ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana mataimakiyar shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin Shen Yueyue, ta halarci bikin rantsar da shugaban kasar a Kinshasa, babban birnin jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a ranar 20 ga watan Janairu. A jiya Lahadi ranar 21 ga wata kuma, shugaba Tshisekedi ya gana da madam Shen Yueyue a Kinshasa.

A yayin ganawarsu, madam Shen Yueyue ta isar da sakon gaisuwa da fatan alheri da shugaba Xi Jinping ya yi ga Tshisekedi. Tana mai cewa, kasar Sin na mai da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Kongo Kinshasa, kuma a shirye take ta yi aiki tare da Kongo Kinshasa wajen aiwatar da muhimman ra’ayoyin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da nuna goyon baya ga juna kan muhimman muradunsu, da zurfafa hadin gwiwa irin na samun moriyar juna da cin nasara tare, da kuma ciyar da sada zumunta a tsakanin jama’ar kasashen biyu, kana da zurfafa yin mu’amala da hadin gwiwa bisa tsarin raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” da na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wato FOCAC, da nufin karfafa kyakkyawar dangantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen Sin da Kongo Kinshasa.

A nasa bangaren, Tshisekedi ya mika godiyarsa ga shugaba Xi Jinping bisa aiko da wakiliya ta musamman don halartar bikin rantsar da shi, ya kuma bukaci Shen Yueyue da ta mika sakon gaisuwa da fatan alheri ga shugaba Xi Jinping. Baya ga haka, Tshisekedi ya jinjina sosai ga ci gaban da aka samu a cikin shirin hadin gwiwa na RFI, wato amfani da ayyukan habaka albarkatu don inganta ayyukan samar da ababen more rayuwa a tsakanin Kongo Kinshasa da Sin. Haka zalika ya bayyana cewa, kasarsa tana mai da hankali sosai kan dadadden zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, tana mai bin manufar Sin daya tak, da kuma fatan zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a wasu muhimman fannoni, ciki har da hakar ma’adinai da dai sauransu, don sa kaimi ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta kai wani sabon matsayi. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaNahiyar AfirkaSinSiyasar Afirka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta shirya Kaddamar Da Shirin Baiwa Dalibai Bashi 

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

4 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

5 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

6 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

7 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

8 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

9 hours ago
Next Post
Tinubu

Gwamnatin Tarayya Ta shirya Kaddamar Da Shirin Baiwa Dalibai Bashi 

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.