• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

by CGTN Hausa
2 years ago
Kongo

LABARAI MASU NASABA

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Bisa gayyatar da shugaba Félix-Antoine Tshisekedi Tshilombo na Jamhuriyar Demokaradiyyar Kongo ya yi mata, wakiliyar musamman ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, kana mataimakiyar shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar Sin Shen Yueyue, ta halarci bikin rantsar da shugaban kasar a Kinshasa, babban birnin jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a ranar 20 ga watan Janairu. A jiya Lahadi ranar 21 ga wata kuma, shugaba Tshisekedi ya gana da madam Shen Yueyue a Kinshasa.

A yayin ganawarsu, madam Shen Yueyue ta isar da sakon gaisuwa da fatan alheri da shugaba Xi Jinping ya yi ga Tshisekedi. Tana mai cewa, kasar Sin na mai da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Kongo Kinshasa, kuma a shirye take ta yi aiki tare da Kongo Kinshasa wajen aiwatar da muhimman ra’ayoyin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, tare da nuna goyon baya ga juna kan muhimman muradunsu, da zurfafa hadin gwiwa irin na samun moriyar juna da cin nasara tare, da kuma ciyar da sada zumunta a tsakanin jama’ar kasashen biyu, kana da zurfafa yin mu’amala da hadin gwiwa bisa tsarin raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” da na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, wato FOCAC, da nufin karfafa kyakkyawar dangantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen Sin da Kongo Kinshasa.

A nasa bangaren, Tshisekedi ya mika godiyarsa ga shugaba Xi Jinping bisa aiko da wakiliya ta musamman don halartar bikin rantsar da shi, ya kuma bukaci Shen Yueyue da ta mika sakon gaisuwa da fatan alheri ga shugaba Xi Jinping. Baya ga haka, Tshisekedi ya jinjina sosai ga ci gaban da aka samu a cikin shirin hadin gwiwa na RFI, wato amfani da ayyukan habaka albarkatu don inganta ayyukan samar da ababen more rayuwa a tsakanin Kongo Kinshasa da Sin. Haka zalika ya bayyana cewa, kasarsa tana mai da hankali sosai kan dadadden zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, tana mai bin manufar Sin daya tak, da kuma fatan zurfafa hadin gwiwa da kasar Sin a wasu muhimman fannoni, ciki har da hakar ma’adinai da dai sauransu, don sa kaimi ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ta kai wani sabon matsayi. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou
Daga Birnin Sin

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Next Post
Tinubu

Gwamnatin Tarayya Ta shirya Kaddamar Da Shirin Baiwa Dalibai Bashi 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.