• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Tasiri Sabbin Karfin Ci Gaban Kasar Sin Za Su Yi Ga Duniya?

by Sulaiman and CGTN Hausa
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wane Tasiri Sabbin Karfin Ci Gaban Kasar Sin Za Su Yi Ga Duniya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin da ake ciki, “Sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko”, ya zamo jumlar da ake yawan ji a fannin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin. Cikakken zaman 3 na kwamitin kolin JKS na karo na 20, wanda aka kammala a baya-bayan nan, ya fitar da matakan zurfafa sauye-sauye a dukkanin fannoni, wanda hakan ke bukatar kyautata tsari, da dabarun raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, daidai da halayen da ake ciki a gida. 

Masu fashin baki sun yi amannar cewa, wannan mataki na nuna irin dagewar kasar Sin, a fannin zurfafa sauye-sauye masu alaka da samar da tsari na shukawa, da bunkasawa, da rayawa sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, ta yadda za a kara azama kan cimma nasarar samun bunkasuwa mai inganci, da ingiza salon zamanantarwa irin ta Sin.

  • MDD Ta Nemi A Gaggauta Cimma Muradun Ci Gaba Mai Dorewa Don Cimma Burin 2030  
  • Sin Na Matukar Adawa Da Shigar Japan Atisayen Soji Na Hadin Gwiwa Da Yankin Taiwan 

Tsohon mataimakin babban sakataren MDD Erik Solheim, ya jinjinawa kokarin kasar Sin na zurfafa sauye-sauye, da kara azamar raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko. Ya yi imanin cewa, amfani da kimiyya da fasaha a matsayin jagora, da nacewa neman ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, su ne jigon nasarar kasar Sin a wannan karni na 21.

A matsayinta na kasuwa ta daya a duniya a fannin cinikayyar makamashi mai tsafta, da sarrafa kayayyakin aikin masana’antu, Sin ta ci gaba da samarwa duniya hajoji masu matukar inganci, kana ta karfafa cimma nasarar sauyin da duniya ke yi zuwa ga ayyuka marasa gurbata muhalli, da masu fitar da karancin iskar carbon. A baya-bayan nan, an yi nasarar sanya hannu kan kwangilar aikin adana makamashi mafi girma a duniya, tsakanin katafaren kamfanin sabon makamashi na kasar Sin wato Sungrow da kamfanin Algihaz na kasar Saudiyya, wanda hakan ke dada nuni ga yadda ci gaba mai inganci na kasar Sin ke amfanar da duniya baki daya.

Abu ne a zahiri, cewa yayin da Sin ke kara zurfafa sauye-sauye a dukkanin fannoni, sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko zai kara zaburar da bunkasuwa, da yaukaka ci gaba mai inganci, da salon Sin na zamanantarwa, da ingiza sabon karsashi ga ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Kasar Tsibiran Solomon: Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Sa Kaimi Ga Farfado Da Tattalin Arzikin Kasar

Next Post

Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

Related

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

7 minutes ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

15 minutes ago
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 
Daga Birnin Sin

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

2 hours ago
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

22 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

23 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

24 hours ago
Next Post
Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

LABARAI MASU NASABA

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

June 5, 2025
Malta Guinness

Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness

June 5, 2025
Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.