• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi: Manufar Sin Daya Tak A Duniya Ce Ta Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi: Manufar Sin Daya Tak A Duniya Ce Ta Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya bayyana a jiya cewa, manufar kasar Sin daya tak a duniya, ita ce ta tabbatar da zaman lafiya a mashigin tekun Taiwan.

Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da aka tambaye shi, kan musabbabin tashin hankalin da ake fama da shi a mashigin tekun Taiwan da kuma yadda za a wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun na Taiwan, yayin da ya gabatar da jawabi game da manufofin kasar Sin game da nacewa kan bude yankin tare da amsa wasu tambayoyi a sakatariyar kungiyar kasashen ASEAN.

  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dauki Jerinta Da Muhimmanci

Da yake jaddada cewa, batun yankin Taiwan shi ne ginshikin babbar moriyar kasar Sin.

Wang Yi ya bayyana cewa, kiyaye ikon mulkin kasa da cikakkun yankuna, wani nauyi ne da ya rataya a wuyan duk wani Basine, kuma babu wani mutum, ko karfi ko wata kasa da za ta yi mafarkin raba yankin Taiwan da kasar Sin.

Wang ya ce, a baya-bayan nan, kasar Amurka ta sha jaddada cewa, za ta kiyaye ‘yancin kai da kuma yankunan kowace kasa, kuma kasar Sin tana mai da hankali sosai, kan yadda take martaba ka’idojin dangantakar kasa da kasa da manufofin MDD.

Labarai Masu Nasaba

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Amma Wang Yi ya bayyana cewa, bisa la’akari da tarihin Amurka, a gefe guda, dole ne a jaddada cewa, bai kamata Amurka ta rika nuna fuska biyu, da yin kwangaba-kwan baya, da kuma sauya matsayinta ba.

A jawabin nasa, Wang ya ce, yankin Asiya yana cikin wani sabon matsayi na tarihi, yana kuma fuskantar damar samun ci gaba da ba a taba ganin irinsa ba. Kasar Sin ta zabi yin hadin gwiwa da mambobin kungiyar ASEAN da sauran kasashen yankin, don tsayawa tsayin daka kan manufar samun zaman lafiya, da ci gaba, da ‘yancin kai da kuma damawa da kowa.
Wang Yi ya ce, kamata ya yi kasashen Sin da Amurka, su kulla kyakkyawar mu’amala a yankin Asiya da tekun Pasifik. Yayin da aka tambaye shi game da yunkurin da Amurka da sauran kasashe ke yi na karfafawa da fadada karfinsu a yankin kuwa.

Ya jaddada cewa, babu wani abin kirki da ya wuce kasashen Sin da Amurka su cimma kyakkyawar mu’amala a yankin, wanda ba wai kawai zai taimaka wajen kara kyakkyawar fata ga kasashen biyu ba, har ma zai gamsar da tsammanin da baki dayan kasashen yankin ke yi. (Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Rashin Tsaro: Ba Za Mu Kara Cewa Buhari Uffan Ba – ACF

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

Related

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

5 hours ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

14 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

16 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

18 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

19 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

LABARAI MASU NASABA

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

August 7, 2025
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

August 7, 2025
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.