Wani abin takaici ya afku a Kawon Alhaji Sani, Layin Mai Unguwa a karamar hukumar Nasarawa, Kano, inda wani matashi mai suna Muhd Sagir mai shekaru 33 ya rasa ransa bayan ya fada cikin wata tsohuwar rijiya da yammacin ranar Laraba.
A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi ya fitar, an samu kiran gaggawa da misalin karfe 12:42 na rana. A ranar 4 ga Yuni, 2025, daga Sabi’u Muhammad, wanda ya ruwaito lamarin.
- ‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi
- Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma
Abdullahi ya ce, jami’an hukumar na gaggawar, nan take suka kai dauki, kuma da isar su, masu aikin ceton sun gano cewa, wanda ya fada rijiyar, mazaunin Kawon Arewa ne, ya fada can cikin tsohuwar Rijiyar da aka daina amfani da ita.
Abdullahi ya ce, an dauko wanda ya fadan a sume amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsa.
Ya kara da cewa, an mika gawar marigayin ga Hakimin Kawon Arewa, Alhaji Hamisu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp